Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani
Published: 24th, November 2025 GMT
Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Kwamred Shehu Sani, ya ce umarnin Shugaba Tinubu na janye ’yan sanda daga gadin manyan mutane zai iya zama magana kawai babu aiki.
A daidai wannan lokaci na ƙara yawaitar rashin tsaro, Shugaba Tinubu ya ce yana sa ido sosai kan al’amuran tsaro a faɗin ƙasa tare da jajircewa wajen kare ’yan Najeriya.
A wani taro da ya yi da hukumomin tsaro a ranar Lahadi, Shugaban Ƙasa ya bayar da umarnin cewa a janye ’yan sanda da ke gadin manyan mutane.
A cewar mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, daga yanzu rundunar ’yan sanda za ta mayar da jami’anta kan ayyukan tsaro na asali.
Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwanaUmarnin ya kuma bayyana cewa duk wani babban mutum da ke buƙatar tsaro zai nemi jami’an hukumar tsaron fararen kaya (NSCDC).
Sai dai a martaninsa a shafinsa na X, Sanata Sani ya nuna damuwa cewa wannan umarni na iya zama magana kawai ba tare da cikakken aiwatarwa ba.
Ya rubuta cewa: “Janye ’Yan Sanda daga manyan mutane ra’ayi ne mai kyau da kuma kyakkyawan tsari duba da gaggawar buƙatun tsaron ƙasa, amma zai iya farawa kuma ya ƙare a matsayin magana kawai.”
Najeriya ta sake fuskantar tashin hankali, ciki har da hare-haren Boko Haram a Borno da kuma farmakin ’yan bindiga a jihohin Kebbi, Neja, Kwara da Borno da Bauchi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda manyan mutane Tsaro manyan mutane magana kawai yan sanda da
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
Shugaban Cocin Katolika reshen Kontagora, ƙarƙashin ya ce ɗalibai 88 da aka yi zaton sun tsere yayin harin da ’yan ta’adda suka kai a makarantar St Mary Secondary School da ke Papiri, ƙaramar hukumar Agwara ta Jihar Neja, har yanzu ba a san inda suke ba.
A cewar majiyoyi, iyaye da dama sun garzaya makarantar domin kwashe ’ya’yansu bayan harin, amma ba ba su yaran ba.
A baya Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindiga sun kutsa cikin makarantar da daddare a ranar Juma’a, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da ma’aikatan makarantar.
Shugaban Cocin Katolika ta Kontagora, Mai Girma Bishop Bulus Dauwa Yohanna, ya sanar ta hannun mai taimaka masa, Daniel Atori, cewa an yi garkuwa da ɗalibai 303, malamai mata huɗu da malamai maza takwas a yayin harin.
Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
Ya ce makarantar na da ɗalibai 430 a ɓangaren firamare, da kuma ɗalibai 199 a ɓangaren sakandare.
Bishop ɗin ya ƙaryata zargin da Sakataran Gwamnatin Jihar Neja ya yi cewa gwamnati ko jami’an tsaro sun yi wa makarantar gargaɗi tun kafin harin.
Ya ce, “Mun tambayi Sakataren Ilimi ko ya samu wata takarda daga gwamnati, ya ce babu; ko an ce ya tura mana wata sanarwa, ma babu. Mun tambaye shi ko an sanar da shi a baki, ya ce a’a. To su faɗa wa duniya wa suka bai wa wannan takarda, ko ta wane hanya aka turo ta?
“Mun kuma tambayar Ƙungiyar Makarantu Masu zaman kansu ta Ƙasa, suma ba su samu wata irin sanarwa ba. Suka ce makarantar an rufe ta kuma an sake buɗe ta kwanaki kaɗan da suka gabata — wannan ma ba gaskiya ba ne. Mu masu bin doka ne,” in ji shi.