Aminiya:
2025-11-24@11:30:07 GMT

Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno

Published: 24th, November 2025 GMT

Mayaƙan Boko Haram masu biyayya ga Ali Ngulde sun fille kan mata biyu a yankin Dutsen Mandara, Gwoza (Borno), bayan sun zarge su da yin shirka.  

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa ƙungiyar kama matan ne da layu a lokacin bincike, inda a bidiyo da suka fitar, mayakan suka ce hakan shaida ce ta bin hanyar da suka kira haramtacciya.

An kai matan zuwa tsaunuka, aka aiwatar da hukunci a bainar jama’a domin tsoratar da mutane da kuma tilasta bin koyarwar ƙungiyar.

Rahotanni sun nuna cewa ɓangaren Ali Ngulde ya ƙara tsaurara matakan hukunci a ’yan watannin nan, inda ake kai hare-hare kan mutanen da ake zargi da sihiri, leƙen asiri, ko kuma yunkurin tserewa.

Sace ɗalibai: Idan ba zai iya ba ya sauka kawai— PDP Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Kwamred Shehu Sani, ya ce umarnin Shugaba Tinubu na janye ’yan sanda daga gadin manyan mutane zai iya zama magana kawai babu aiki.

A daidai wannan lokaci na ƙara yawaitar rashin tsaro, Shugaba Tinubu ya ce yana sa ido sosai kan al’amuran tsaro a faɗin ƙasa tare da jajircewa wajen kare ’yan Najeriya.

A wani taro da ya yi da hukumomin tsaro a ranar Lahadi, Shugaban Ƙasa ya bayar da umarnin cewa a janye ’yan sanda da ke gadin manyan mutane.

A cewar mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, daga yanzu rundunar ’yan sanda za ta mayar da jami’anta kan ayyukan tsaro na asali.

Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana

Umarnin ya kuma bayyana cewa duk wani babban mutum da ke buƙatar tsaro zai nemi jami’an hukumar tsaron fararen kaya (NSCDC).

Sai dai a martaninsa a shafinsa na X, Sanata Sani ya nuna damuwa cewa wannan umarni na iya zama magana kawai ba tare da cikakken aiwatarwa ba.

Ya rubuta cewa: “Janye ’Yan Sanda daga manyan mutane ra’ayi ne mai kyau da kuma kyakkyawan tsari duba da gaggawar buƙatun tsaron ƙasa, amma zai iya farawa kuma ya ƙare a matsayin magana kawai.”

Najeriya ta sake fuskantar tashin hankali, ciki har da hare-haren Boko Haram a Borno da kuma farmakin ’yan bindiga a jihohin Kebbi, Neja, Kwara da Borno da Bauchi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani
  • Najeriya: Kungiyar Yan Ta’adda Ta ISWAP Ta Sace Yan Mata 13 A Jihar Borno
  • ISWAP ta sace ’yan mata 13 a Borno
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
  • NAJERIYA A YAU: Ba A Yi Ma Nnamdi Kanu Adalci Ba- Emmanuel Kanu
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi