Aminiya:
2025-11-27@06:57:04 GMT

Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka

Published: 27th, November 2025 GMT

An kulle Fadar Shugaban Kasar Amurka ta White House tare da wasu gine-ginen gwamnati da dama, sakamakon harbin ɗan bindigar da ya raunata sojoji biyu a kusa da fadar.

A yayin, an harbe masu tsaron fadar biyu har lahira.

Gwamna Patrick Morrisey da farko ya ce an kashe sojojin, amma daga baya ya ce yana samun “rahotanni masu karo da juna” game da halin da suke ciki, yana mai da cewa za a fitar da ƙarin bayani idan an tabbatar.

A cikin wani rubutu a shafin X, ya ce, “Yanzu muna samun rahotanni masu cin karo da juna game da halin sojojin biyu, kuma za mu bayar da ƙarin bayani idan mun samu cikakken rahoto.

“Addu’o’inmu suna tare da waɗannan jarumai, iyalansu, da dukan al’ummar Amurka.”

A cewar rahotanni, Shugaba Donald Trump yana gidansa na hutu a Mar-a-Lago da ke Palm Beach, Florida, a lokacin da lamarin ya faru.

Mai magana da yawun Fadar White House, Karoline Leavitt, ta ce cikin wata sanarwa: “Fadar White House ta san da wannan mummunan lamari kuma tana bin diddigi. Shugaban kasa ya samu cikakken bayani.”

’Yan sandan birnin Washington DC sun ce an kama wanda ake zargi da harbin.

Sojojin National Guard sun kasance a Washington DC tsawon watanni a matsayin wani bangare na matakin Trump na yaki da laifuka a babban birnin ƙasar.

A cikin wani rubutu a dandalinsa na Truth Social, Trump ya ce: “Dabban da ya harbi mambobin National Guard biyu, wanda dukkansu suka ji rauni mai tsanani kuma yanzu suna a asibitoci daban-daban, shi ma ya ji rauni sosai, amma duk da haka, zai ɗanɗana kuɗarsa.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya

An naɗa Andrea Thompson, ’yar ƙasar Birtaniya, a matsayin mace mafi ƙarfi a duniya.

Wannan na zuwa ne bayan tabbatar da cewa wanda aka bayyana a matsayin zakara — Jammy Booker — tun da farko namiji ne da aka sauya masa halitta zuwa mace, lamarin da ya sa aka soke nasararsa bisa saɓawa dokokin gasar.

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai

Thompson mai shekaru 43, ta karɓi lambar yabon ne daga masu shirya gasar nunin ƙarfi ta duniya, kwanaki biyu bayan kammala bikin a Arlington da ke birnin Texas na Amurka, wanda aka gudanar a daga 20 zuwa 23 ga watan Nuwamba.

Gasar nuna ƙarfin ta duniya tana da tsauraran ƙa’idoji, inda ake bai wa ’yan takara damar fafatawa ne kawai bisa jinsinsu na asali domin tabbatar da adalci.

A gasar bana, Thompson ta ƙare a matsayi na biyu bayan kammala fannonin wasanni guda shida da suka haɗa da ɗaga nauyi da sauran gwaje-gwaje a rukunin mata.

Lokacin da aka ayyana Jammy Booker a matsayin zakara gabanin a gano namiji ne ya sauya jinsi

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
  • Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
  • Iran Ta Mika Ta’aziyyarta Ta Shahadar Wani Kwamanda Na Mayakan Hizbullah