Ya yi nuni da rahoton 2021 da Cibiyar Binciken kasa ta Nijeriya ta fitar, wanda ya gano kimanin filaye da gine-ginen gwamnatin tarayya 11,866 da aka yi watsi da su a duk faɗin ƙasar.

 

Daga cikin manyan kadarorin da ɗan majalisar ya lissafa akwai Cibiyar Sakatariyar Tarayya da ke Ikoyi, Legas; Ginin Otal na Ƙasa da Ƙasa na Nijeriya, Suleja, Jihar Neja; Millennium Tower, Abuja; Ginin Hukumar Haraji ta Tarayya a Jihar Abia; Hedikwatar Dakin karatu na Ƙasa, Abuja; Kamfanin Masana’antar buga Labarai na Nijeriya, Kaduna; Ginin Masaƙa ta Kaduna; da Kamfanin Narka Alluminium na Nijeriya, Jihar Delta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule November 13, 2025 Manyan Labarai Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista November 12, 2025 Manyan Labarai An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano November 12, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: na Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar

Daga Usman Muhammad Zaria 

 

Ministan Yada Labarai Alhaji Mohammed Idris, ya yabawa Gwamna Malam Umar Namadi bisa jagoranci na gaskiya da tsari, yana mai cewa Jihar Jigawa ta zama abin koyi wajen gudanar da mulki da kuma ingantaccen aiki a ma’aikatu.

Ministan ya yi wannan yabo ne lokacin wata ziyarar ban girma da ya kai wa gwamnan a Gidan Gwamnati da ke Dutse.

Muhammad Idris ya tuna da wata ziyarar da ya taba kaiwa Jigawa a baya, lokacin da ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya domin duba harkokin noma. Ya ce yadda ya ga ana yin noman rani ya sa shi shauki game da irin ci gaban da ake samu a jihar.

Ya kuma bayyana godiyarsa kan kyakkyawan tarba da tawagarsa ta samu, yana mai cewa Jigawa jiha ce mai mutunci, zumunci da karimci.

Ministan ya kara tabbatar da aniyar gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wajen magance matsalolin tsaro da tattalin arziki, musamman ta hanyar gyaran da ake yi a rundunar tsaro domin tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya yi maraba da ministan da tawagarsa, yana mai bayyana cewa taron matasan APC na Arewa maso Yamma wata dama ce ta musayar ra’ayi game da mulki, ci gaba da kuma bunkasar matasa.

Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen bunkasa karkokin matasa da mata a cikin tsarin shirye shiryenta na cigaban jihar.

“Muna goyon bayan mulikin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, Mutanen Jigawa suna tare da shi, muna goyon bayan shirin sa na ‘Renewed Hope’ domin gina Najeriya mai da hadin kai,” in ji gwamnan.

Daga nan sai gwamnan tare da ministoci suka halarci taron matasan APC na Arewa maso Yamma a Dutse, inda aka tattauna batutuwan shugabanci, gudunmawar da matasa ke badawa, da ci gaba mai dorewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a
  • Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka
  • An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano
  • Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
  • Bayan Da Muka Fara Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Ka’idoji Ga Samar da Injinan Noma a Najeriya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar
  • Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump