Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya
Published: 25th, November 2025 GMT
Shugaban kasar Sudan kuma babban kwamandan sojojin kasar Janar Abdulfattah Alburhan, ya yi watsi da shawarar Amurka ta kawo karshen yaki a kasarsa wanda ya lakume rayukan mutane da dama, ya kuma raba kasar gida biyu a cikin watanni kimani 30 da suka gabata.
Shafin yanar gizo na labarai ‘AfricaNews’ ya nakalto Burhan yana fadar haka a ranar Lahadi jim kadan bayan ganawarsa da tawagar kasar Amurka wacce ta gabatar masa da shawarar, ya kuma bayyana ta a matsayin mafi munin shawarar tsagaita budewa juna wuta da aka gabatar masa ya zuwa yanzun.
Burhan ya zargi Amurka da goyon bayan yan tawayen a cikin shawarar da ta gabatar, kuma shawarar ba irin zaman lafiyan da mutanen sudan suke so ba. Masana suna ganin gwamnatin Amurka da kawayenta wadanda suke goyon bayan yantawaye a duniya musamman a cikin kasashen Larabawa suna son sake raba kasar Sudan ne, kuma sun gabatar da wannan shawarar ce a dai-dai lokacinda suka fahinci cewa gwamnatin kasar tana samun nasara a kan yan tawaye wadanda suke iko da yankin Darfur na yammacin kasar ta Sudan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji November 24, 2025 Habasha: Bayan Shekaru 10,000 Dutsen Hayli Gubbi Ya Yi Aman Wuta November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Venezuela Ta Gargadi Amurka Kan Shirin Tada Hankali A Kan Iyakokin Kasar
Gwamnatin kasar Venezuela ta gargadi kasar Amurka kan duk wani shirin kifar da gwamnatin shugaba Nicolas Madoro, a dai-dai lokacin da gwamnatin Trump take bada wani sabon yunkuri nan kusa na ganin ta kwace iko da kasar Venezuela, ta kuma raba Madoro da shugabancin kasar.
Kafafen yada labarai da dama sun nakalto manya-manyan Jami’an gwamnatin shugaba Trump suna fadar cewa sojojin kasar suna shirin kaddamar da hare-hare kan kasar Venezuela nan ba da dadewa ba, don ganin sun kwace ikon kasar daga hannun shugaba Madoro.
Sai dai mamu sanya ido a kan abubuwan da ke faruwa a kusa da kasar Venezuela sun bayyana cewa, gwamnatin Amurka ta tura kataparen jiragen daukar jiragen yaki wato Carier, da wasu jiragen yawan yaki dauke da jiragen yaki samfurin F35 da kuma sauran kayakin yaki zuwa kusa da kasar ta Venezuela a cikin tekun Carebian, da sunan yaki da safarar miyagun kwayoyi wanda Washington tace madoro ne yake jagorantar su.
Sun ce ba dole ne Amurka ta sami nasarar sauke madoro a kan kujerar shugabancin kasar ba. Hukumar CIA wacce shugaba Trump ya azawa nauyin sauke Madoro da kuma ita fadar white house basu ya maganar yauce da kuma yadda juyin mulkin zai kasance ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka CAN: Yawan Yaran Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Ranar Jumma’a Sun Fi 300 November 23, 2025 Ribadu Ya Gana da Sakataren Yakin Amurka Kan Batun Kashe Kiristoci A Nijeriya November 22, 2025 Daliban Jami’ar st Gorges Ta Birnin London Sun yi Zanga-zangar Nuna Adawa Da Daukar Tsohon Sojan Isra’ila Aiki November 22, 2025 Isra’ila Ta Kashe Yara Falasdinawa Guda 22 A Yankin Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta November 22, 2025 Iran Ta Sanar Da Nada Janar Jahanshashi A Matsayin Kwamandan Dakarun Rudunar Sojin Kasa November 22, 2025 Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Bukaci shugaba Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000 November 22, 2025 Nijar: Dubban Mutane Sun Tarbi Janar Thiani Bayan Komarwa Birnin Yamai November 22, 2025 Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba November 22, 2025 Rundunar Sojan Iran Tana Cikin Shirin Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana November 22, 2025 Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka November 22, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci