Aminiya:
2025-11-26@19:59:28 GMT

Real Madrid za ta yi karon-batta da Olympiacos a Gasar Zakarun Turai

Published: 26th, November 2025 GMT

A yammacin nan ne ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid za ta kece raini da Olympiacos a ci gaba da Gasar Zakarun Turai, duk da rashin wasu manyan ’yan wasanta biyu.

Babban mai tsaron ragar Madrid, Thibaut Courtois, da ɗan wasan baya Dean Huijsen, na fama da jinya, lamarin da zai hana su buga wannan muhimmin wasa.

Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu

Yanzu haka jerin ’yan wasan Madrid da ke jinya sun haɗa da: Thibaut Courtois, Dean Huijsen, Antonio Rüdiger, David Alaba, Franco Mastantuono, da Éder Militão.

Tun bayan zuwan sabon kocin Real Madrid, Xabi Alonso, Courtois ya riƙe ragamar tsaron raga a dukkan wasanni 17 da suka buga a kakar nan.

Andriy Lunin, ɗan asalin ƙasar Ukraine mai shekaru 26, shi ne mai tsaron da ya fi samun damar buga wasanni a zamanin tsohon koci Carlo Ancelotti, lokacin da Courtois ya yi jinya mai tsawo.

Gasar Zakarun Turai dai fage ne da Real Madrid ta yi fice a duniya wadda ta lashe sau 15 a tarihi.

A bana, ƙungiyar tana da maki 9 daga wasanni 4 da ta buga zuwa yanzu da ake kece raini a matakin rukuni

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gasar Zakarun Turai

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe ta ƙaddamar da sabbin matakan ƙarfafa tsaro a makarantu bayan wani taron tattaunawa da aka gudanar tsakanin Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Bello Yahaya, da shugabannin Ƙungiyar Malaman Sakandare reshen jihar.

An gudanar da taron ne a Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe, bisa umarnin Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, na ƙara tsaurara tsaro a makarantu a faɗin ƙasar nan.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya bayyana cewa tattaunawar ta mayar da hankali kan duba tsarin tsaro na yanzu a makarantu, musamman waɗanda ke yankunan da ke da ƙalubale, tare da gano wuraren da ake buƙatar gaggawar gyara.

CP Bello Yahaya ya tabbatar da kudirin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya na ci gaba da kare cibiyoyin ilimi, yana mai cewa makarantu dole ne su kasance wurare masu aminci domin koyo da koyarwa.

Ya jaddada muhimmancin yin nazarin tsaro a kai a kai, tsara matakan rigakafi, da kuma tabbatar da ci-gaba da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin makarantu, Ma’aikatar Ilimi da hukumomin tsaro.

Kwamishinan ya bayyana cewa rundunar ta ƙara karfafa sintiri, sa ido, da kuma gaggawar amsa kira a yankunan makarantu da aka fi ganin haɗarin tsaro.

Ya kuma bukaci shugabannin makarantu su riƙa kasancewa a shirin tuntuɓar ofisoshin ’yan sanda mafi kusa, tare da hanzarta ba da rahoton duk wani abin da ya haifar da zargi.

Ya yaba wa shugabannin ANCOPSS bisa jajircewarsu wajen aiki tare da hukumar ’yan sanda domin ƙarfafa tsaro a makarantu.

A nasu ɓangaren, shugabannin ANCOPSS sun gode wa rundunar ’yan sanda bisa ƙoƙarin da take yi na tabbatar da lafiyar dalibai da malamai, tare da alƙawarin yin aiki kafada da kafaɗa da rundunar da Ma’aikatar Ilimi domin ƙarfafa duk tsare-tsaren tsaro a makarantun sakandare.

Rundunar ta kuma yi kira ga iyaye, malamai, shugabannin al’umma, da mazauna unguwanni da su kasance masu lura da faɗakarwa, tare da tallafa wa duk wani yunƙurin inganta tsaro a makarantu, domin kiyaye rayuwar ɗalibai nauyi ne da ya rataya a kan kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000