Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano
Published: 15th, November 2025 GMT
Wasu mahara sun yi wa wasu matan aure biyu kisan gilla a gidan mijinsu da keunguwar Tudun Yola a Ƙaramar Hukumar Gwale ta Jihar Kano.
Aminiya ta samu rahoton cewa maharan banka wa gidan wuta bayan da suka soka wa ɗaya daga cikin matan wuka har lahira, ɗayar kuma an tsinci gawarsa a cikin banɗaki.
Matan da aka yi wa wannan kisan gilla — Hauwa’u Yakubu da Zahra’u Aliyu — mata ne ga wani mai suna Alhaji Ashirin Shu’aibu Usaini.
Al’unnar unguwar Tudun Yola sun shiga tashin hankali da wannanan ɗanyen aiki.
HOTUNA: Yadda Babban Taronjam’iyyar PDP ke gudana Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a BornoƊan mai gidan, Anas Shu’aibu, ya yi zargin ana yi wa matan mahaifinsa wannan kisan gilla ne da tsakar rana lokacin da mai gidan da ’ya’yansa suka fita.
“Ba mu san abin da ke faruwa ba sai da daddare bayan mahaifinsmu ta kira cewa ina dawo gida, muna zuwa muka ga ɗaya yaqar a ƙone, ɗayar muka an kulle ta a banɗaki, ko da muka ɓalle ƙofar sai muka samu ita ma ta riga ta mutu.
“Da farko mun yi zargin gobara ce, amma sai muka lura cewa da alamar hari aka kai musu.”
Alhaji Shu’aibu, cikin kaɗuwa ya bayyana cewa “sun kashe Matana, sun ƙona gawar ɗayar. Ban san dalilin wannan rashin imani ba.”
Kakakin ’yan sandan Jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Koyawa ya tabbatar da faruwar lamarin tare da cewa rundunar ta ta fara gudanar da bincike a kai.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
’Yan banga 16 sun kwanta dama a yayin da ’yan bindiga suka yi garkuwa da mutane 42 a wani hari na daban a Ƙaramar Hukumar Mashegu da ke Jihar Neja.
Aminiya ta samu rahoton cewa ’yan bindiga sun kai hare-haren ne daga ranar Alhamis zuwa Asabar, lamarin da ya sa mutane da dama yin ƙaura daga ƙauyuka
Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa maharan sun fara kai farmaki ne a ƙauyen Dutsen Magaji, inda suka yunwa mutane 22 kisan gilla.
“Da suka kawo hari, ’yan banga sun bi su, ɓangarorin suka yi musayar wuta, amma suka kashe ’yan Banda biyar, wasu uku na karɓar magani a Asibiti.”
Ya ce daga baya ’yan bindiga suka kawo sabon hari da asuba, ranar Alhamis a yayin da ake Sallar Asuba a ƙauyen Magama, suka yi garkuwa da mutane 20.
“Nan ma da ’yan bindiga suka bi su, ashe sun yi kwanton ɓauna, suka kashe ’yan banga 13, suka jikkata wasu da dama.”
Sakataren Yaɗa labaran Shugaban Ƙaramar Hukumar Mashegu, Isah Ibrahim Bokuta, ya tabbatar da hare-haren, tare da jinjina wa ’yan bangar bisa yadda suka sadaukar da ransu domin kare al’umnarsu.
Wakilinmu ya yi ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun ’yan sanda na Jihar Neja, Wasiu Abiodun, amma ya ce zai tuntuɓe shi daga baya, idan ya bincika.
A gefe guda, mazauna yankin sun shaida mana cewa tun ranar Litinin al’ummomi da dama sun yi gudun hijira zuwa Mashegu, Kawo-Mashegu, Manigi da wasu wurare. Wasu kuma sun fake a gidajen ’yan uwansu a nesa domin tsira.
Majiyoyi sun ce cikin ƙauyukan da aka watse har da Dutsen Magaji, Borin Aiki, Gidan Ruwa da Magama.
Hakazalika har yanzu masu garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar SUBEB ta Jihar Neja, Alhaji Alhassan Bawa Niworo, ba su sake shi ba, makonni bayan rahoton cewa iyalansa sun biya kuɗin fansa na Naira miliyan 70.
An yi garkuwa da Niworo ne a ranar Litinin, 29 ga Satumba, 2025, tare da Kwamishina na Dindindin II na Hukumar Zaɓe ta Jihar Neja (NSIEC), Barrister Ahmad Mohammed, direbobinsu da wasu matafiya a kan titin Mokwa–New Bussa, a Karamar Hukumar Borgu.