Leadership News Hausa:
2025-11-14@07:31:26 GMT

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Published: 14th, November 2025 GMT

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

A bisa wannan dalilin, ya kuma zama waji, manyan hafsohin tsaron su mayar da hankali, wajen ingnata jin dadi da walwalar dakarun sojin, musamman duba da cewa, manyan hafsoshin tsaron, su ba baki ne, kan wadannan kalubalen ba, domin kuwa kafin nada su, a baya an nada su kan makamai da ban da ban.

Kwarewar da kuma ilimin da suke da shi, a aikin soji, abu ne da zai taimaka masu wajen sauke nauyin da aka dora masu.

Abu na biyu shi ne, akwai bukatar a tsakaninsu, su hada karfi da karfe, domin su samu nasarar tunkarar aikin da ke a gabasu na tabbatar da tsaro a kasar, ba wai su rinka yi aiki, a daidaikunsu ba.

Kazalika, dole na rundunar sojin sama ta taimaka wa rundunar soji na kasa da kuma na ruwa, a yayin duka wani farmaki, tare da kuma yin musayar bayanai, a tsakansu.

Na ukun shi ne, dole ne su mayar da hankali kan samar dabaru, yayin gudanar da ayyukansu, musamman duba da irin sarkakiyar da ke tattare da yanayin kalubalen rashin tsaron kasar, misali duba da irin salon ayyukan ‘yan bindiga daji da masu garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan ta’adda, na kai hare –hare, wanda a yanayi irin wannan akwai matukar a dauki dabarun magance wannan barazanar ta su.

Yakar ta ‘yan bindiga daji da masu garkuwa da mutane da kuma masu aikata manyan laifuka, ya zarce ace manyan hafsoshin tsaro ne kadai za su yi hakan, domin kuwa, akwai kuma bukatar su tabbatar da sun samu goyon bayan alummar gari, musamman ta hanyar samun bayanan sirri.

Bugu da kari, na hudun shi ne, su tabbatar da dakarunsu na kai farmaki ta kasa duba da cewa, akasarin kalubalen rashin rashin tsaron ya ta’allaka ne na kasa, musamman duba da cewa maboyar ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga daji, a kan doron kasa suke.

Dole ne manyan hafsoshin tsaron su sanya a zuciyarsu na cewa, su masu yin biyayya ne, ga kundun tsarin mulkin kasar kuma dole ne su kare su tabbatar da sun kare dorewar mulkin dimokaradiyyar kasar.

Kazalika, ya zama wajbi, a tantace a tsakanin ayyukan soji na kuma na siyasa.

A saboda haka ne, ba ma goyon bayan soji yin kutse a cikin batun abinda ya shafi fanin siyasa, musamman duba da cewa, kasashen da soji suka shiga cikin lamarin siyasa, sun kasance, ba su ji dadi ba, kuma bai kamata Nijeriya ta kasance a cikin jerin irin wadannan kasashen ba.

Wannan Jaridar na shawartar ‘yan siyasar kasar nan, kar su kutsa kansu kan batun da ya shafi lamuran ayyukan sojin kasar, musamman gwamnonin jihohin kasar, musamman duba da cewa, mun lura da irin wannan shishigin na wasu ‘yan siyasar kasar inda suke bayyana gazawar da sojin kasar ke yi, na tabbatar da tsaro a kasar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4 November 13, 2025 Manyan Labarai Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2 November 13, 2025 Manyan Labarai Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su November 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: musamman duba da cewa tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

 

A jawabinsa, ministan ya bayyana cewa, binciken jin ra’ayin ‘yan kasa a fannin kiwon lafiya da aka gudanar a shekarar 2023, 2024, da 2025 ya nuna sakamako mai karfafa gwiwa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano November 12, 2025 Manyan Labarai Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro November 12, 2025 Manyan Labarai Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau
  • Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista
  • Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina
  • Venezuela: Maduro Ya Sanya Hannu Kan Dokar Tsaron Kasa Mai Cikakkiyar Kariya
  • DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma
  • Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro
  • CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15
  • ‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir