Leadership News Hausa:
2025-11-13@21:55:09 GMT

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Published: 14th, November 2025 GMT

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar kwamitin shirya wasannin Olympics na duniya (IOC), Kirsty Coventry, ta halarci bikin bude gasar wasannin kasa ta Sin karo na 15 a lardin Guangdong da yammacin ranar 9 ga Nuwamba. A ranar 12 ga wata kuma, Coventry ta yi wata hira ta musamman da ‘yar jarida daga babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG a nan birnin Beijing.

Yayin hirar, Coventry ta bayyana cewa, gasar wasannin kasar Sin ta wannan karo tana da babbar ma’ana. Ta ce yayin da take ziyarar aiki a Sin, ta yi tattaunawa da dama, ciki kuma har da ganawa da shugaba Xi Jinping. Shugaba Xi ya ce mokamar bunkasuwar yankin gabar tekun Guangdong-Hong Kong-Macao, ba tsara manufofin da za a iya cimmawa kadai ya yi ba, har ma da gabatar da alkiblar da za ta tabbatar da cimma hakan a karshe. Ta ce tana fatan wasannin za su iya taka rawa mai tasiri da inganci a cikin wannan tsari.

Ta kara da cewa, a yanzu, wasanni sun zama masana’antar duniya mai daraja sosai. Inda ta ce tana matukar farin cikin ganin jari mai yawa ya shiga cikin harkokin gina al’ummomi. Kuma saka hannun jari a bangaren wasanni, a zahiri saka hannun jari ne a cikin al’umma, kuma yana da muhimmanci ga gina zamantakewa mai kuzari.(Safiyah Ma)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya November 13, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu November 13, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya November 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 

A shekarar 2023, Ronaldo, wanda ke taka Leda tare da Al Nassr ta Saudiyya, ya tabbatar da maganar da ya yi na cewa, zai rataye takalminsa nan ba da jimawa ba, “Idan ina nufin nan ba da jimawa ba, watakila shekara daya ko biyu zan ci gaba da kasancewa a wasan,” in ji shi.

 

Ronaldo wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or sau biyar yana da burin buga Kofin Duniya na shida a shekara mai zuwa, ya kusa lashe kofin a shekarar 2006, lokacin da Portugal ta sha kashi a hannun Faransa a wasan kusa da na karshe, a halin yanzu, Portugal ba ta sami gurbi a gasar 2026 ba, wadda za ta gudana a Amurka, Kanada, da Mexico, amma za su iya samun gurbin shiga gasar ta hanyar doke Ireland a ranar Alhamis.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni ‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina November 11, 2025 Wasanni Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL November 9, 2025 Wasanni Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya November 9, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia
  • Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
  • Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
  • Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya
  • Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji
  • ‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026
  • CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15
  • Kofin Duniya 2026 Zai Zama Na Ƙarshe A Wuri Na – Ronaldo 
  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina