Aminiya:
2025-12-13@12:53:30 GMT

Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana

Published: 13th, November 2025 GMT

Aƙalla mutum 12 sun mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata a wani turmutsutsu da ya faru yayin jarabawar ɗaukar aikin soja a Filin Wasa na El-Wak da ke Accra, babban birnin ƙasar Ghana.

Lamarin ya faru ne da safiyar Laraba, yayin da ɗaruruwan matasa masu neman aikin suka kutsa cikin filin wasan ba tare da bin tsarin shiga da aka tanada ba.

An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo

Rundunar Tsaron Ghana (GAF) ta ce mutum shida ne suka mutu a farko, amma rahotanni daga asibitin sojoji sun tabbatar da cewar adadin mamatan ya ƙaru zuwa mutum 12.

Wasu mutum 22 sun jikkata, ciki har da biyar da ke cikin mawuyacin hali, kamar yadda jami’ar asibitin sojojin ƙasar ta tabbatar.

Ministan Tsaro, Dokta Cassiel Ato Forson, ya ce an dakatar da ɗaukar na wani ɗan lokaci tare da kafa kwamiti domin binciken musabbabin lamarin, wanda ta bayyana a matsayin abin takaici.

Shugaban ƙasar, John Mahama, ya kai ziyarar jaje ga iyalan waɗanda suka mutu da kuma marasa lafiya, inda ya bayyana cewa gwamnati za ta ɗauki matakan tabbatar da cewa irin wannan lamari ba zai sake faruwa ba.

Rundunar Tsaron Ghana ta miƙa sakon ta’aziyya ga iyalan da abin ya shafa tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kula da waɗanda suka jikkata a asibitin sojoji.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot

Mai horar da Ƙungiyyar Ƙwallon Ƙafa ta Liverpool, Arne Slot ya ce zai sanya Mohammed Salah cikin jerin ’yan wasan da za su bugawa Liverpool wasa da Brighton a ranar Asabar.

Slot wanda ya samu saɓani da Salah kan ajiye shi a benci a wasanni uku a jere, ya ce yana da yaƙinin cewa, Salah zai ci gaba da bugawa ƙungiyar wasa.

2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya

Ya kuma ƙara da cewa, zai ci gaba da tattaunawa da ɗan wasan domin ya ci gaba da taka leda a Anfield.

Salah mai shekara 33, baya cikin jerin ‘yan wasan da suka doke Inter Milan a Italiya a ranar Talata, wanda hakan ke bayyana tsamin rashin jituwa tsakaninsa da Arne Slot.

Liverpool dai zata karɓi baƙuncin Brighton a wasan mako na 16 da ƙarfe 3 na ranar Asabar.

Mo Salah, ɗan asalin ƙasar Masar, ya bugawa Liverpool wasanni 420 tare da zura ƙwallaye 250 cikin zamansa a ƙungiyyar.

Ɗan wasan zai bar Liverpool domin dawowa ƙasar Masar a ranar 15 ga watan Disamba, kwanaki 6 gabanin fara kofin nahiyyar Afrika da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026
  • Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila
  • Karamar Hukumar Agwara ta Jinjinawa Gwamnati Bisa Tabbatar da Tsaron Rayuka da Dukiyoyin Jama’a
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara