Leadership News Hausa:
2025-11-14@20:13:50 GMT

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

Published: 14th, November 2025 GMT

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

An yi hadaka tsakanin asusun da ke tallafa wa bunkasa aikin noma na kasa (NADF) da kuma Gwamnatin Jihar Jigawa, inda suka kaddamar da shiri na farko na bai wa manoma bashin noma.

A cikin sanawar da asusun ya fitar, shirin zai bayar da dama ga masu zaman kansu, musamman kananan manoma wajen ba su bashin kudin noma tare kuma da kara samar musu da wadataccen abinci.

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4 Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Babban Sakataren Asusun, Mohammed Ibrahim ya bayyana cewa; shirin zai magance gibin da kananan manoma ke fuskanta wajen samun rance kudaden noma.

ADVERTISEMENT

Shi kuwa, Darakta Janar na Hukumar Bunkasa Aikin Noma na Jihar Jigawa, wato JATA Dakta Saifullahi Umar, ya bayar da tabbacin cewa; jihar ta mayar da hankali wajen bunkasa fannin aikin noma ta hanyar yin amfani da fasahar zamani tare da jawo kamfanoni masu zman kansu, ta hanyar yin hadaka.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Noma Da Kiwo Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji November 7, 2025 Noma Da Kiwo An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi November 7, 2025 Noma Da Kiwo Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci November 2, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki

Tsohon shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, ya buƙaci jam’iyyar PDP da ta ɗage babban taronta da ta shirya gudanarwa tsakanin ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamba a birnin Ibadan na Jihar Oyo.

Saraki ya ce ci gaba da shirin gudanar da taron duk da irin umarnin dakatarwa da kotuna suka bayar zai ƙara ta’azzara rikicin jam’iyyar sannan ya jefa ta cikin matsaloli a nan gaba.

An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya Nijeriya za ta kece raini da Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya

Ya bayyana haka ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, bayan karɓar baƙuncin ’yan kwamitin amintattun jam’iyyar ƙarƙashin shugabancin Ambasada Hassan Adamu, a gidansa.

Tawagar ta ziyarci Saraki ne domin neman tabarrakinsa da shawarwari kan yadda za a cimma haɗin kai a jam’iyyar da ta samu rarrabuwar kai.

Tsohon shugaban da ya jagoranci Majalisar Dattawa daga 2015 zuwa 2019, ya ce umarnin kotuna kusan huɗu masu karo da juna game da babban taron zai iya jawo matsala kan halascin duk wani mataki da ya biyo bayan taron.

Zuwa yanzu, akwai ƙararraki uku a gaban kotuna daban-daban waɗanda suka bayar da umarnin dakatar da shirin taron, yayin da PDP ta ce tana ci gaba da shirin gudanar da shi a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.

Daga cikin waɗanda suka kai jam’iyyar kotu kan taron akwai Ministan Abuja, Nyesom Wike, da tsohon Gwamnan Jigawa, Sule Lamido.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani
  • HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya
  • Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki
  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya a Jihar
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Ka’idoji Ga Samar da Injinan Noma a Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Shirya Faɗaɗa Gonakin Shinkafar Jangwa Don Ƙara Samar da Shinkafa