Atiku ya musanta labarin ba sojan da ya yi takaddama da Wike kyautar motar SUV
Published: 13th, November 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya karyata rahotannin da ke cewa ya bai wa Laftanar Ahmed Yerima, sojan ruwan nan da ya samu takaddama da Ministan Abuja, Nyesom Wike, kyautar sabuwar mota kirar Toyota SUV.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar ta shafinsa na X a ranar Alhamis, Atiku ya bayyana labarin da ke yawo a kafafen sada zumunta a matsayin ƙarya tsagwaronta ba tare da wata hujja ba.
Ibe ya bukaci jama’a da su yi watsi da wannan labari da aka ƙirƙira.
“Mai girma Atiku Abubakar, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Najeriya (1999–2007), bai bai wa Laftanar Ahmed Yerima, ko wani mutum ba, sabuwar motar Toyota SUV, sabanin rahotannin ƙarya da ke yawo a kafafen sada zumunta.
“Labarin ƙarya ne gaba ɗaya kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi,” in ji shi.
Zargin da ya fara yawo a Facebook a ranar Laraba ya ce Atiku ya ba da kyautar motar ga sojan ruwa bayan takaddamar da ya samu da Wike kan wani rikicin fili a Abuja.
Takaddamar ta faru ne a ranar Talata lokacin da Wike ya yi arangama da sojan ruwan yayin da yake duba wani fili da ake takaddama a kan shi a unguwar Gaduwa da ke cikin Babban Birnin Tarayya.
Bidiyon lamarin da ya yadu a intanet ya nuna yadda aka yi musaya yawu mai zafi tsakanin ministan da sojan.
Lamarin ya haifar da ce-ce-ku-ce a fadin ƙasa, inda fitattun mutane da dama, ciki har da tsohon Shugaban Rundunar Sojin Ƙasa, Janar Tukur Buratai (mai ritaya), da wasu ’yan siyasa, suka bukaci a kai zuciya nesa kuma a girmama dokokin kasa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahadi A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran
Dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran sun yi musayar wuta da yan ta’adda a kudu masu gabacin kasar, sannan wasu daga cikinsu su sun yi shahada sannan sun halaka yan ta’adda da dama. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na JMI ya dakarun na IRGC guda uku nesuka yi shahada a wannan fafatawar, a jiya Laraba a garinLar da ke kusa da birnin Zahidan babban birnin Lardin. Garin Lar dai yana kan iyakar kasar Iran da Pakisatan, kuma ba wannan ne karon farko wadanda dakarun suke fafatawa da yan ta’adda wadanda suke samun goyon bayan kasashen waje ba. Kuma suke da sansanoninsu a cikin lardin sitan Baluchistan na kasar Pakistan ba.Har yanzun dakarun rundunar Qudus wanda suke aiki a karkashinsu basu bayyana sunayen sojojin da suka yi shahadar ba. Amma sun kaddamarda wata tawaga wacce zata gudanar da binciken gaggawa don gano abinda ya faru.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamsa: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjeniyar Tsagaita Bude Wuta A Yankin December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci