Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
Published: 26th, November 2025 GMT
Sojoji a Guinea-Bissau sun ce sun yi juyin mulki tare da karɓe ragamar mulkin ƙasar.
Sun kuma sanar da dakatar da zaɓukan ƙasar tare da rufe iyakokinta nan take.
’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSSWannan na zuwa ne kwana uku bayan ƙasar ta gudanar da zaɓen ’yan majalisa da na shugaban ƙasa.
A yau ne aka wayi gari ana ji. harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa, lamarin da ya tashi hankalin mutane.
Daga bisani kuma dakarun soji suka rufe babban titin da ke zuwa fadar shugaban ƙasar.
A cewar majiyar AFP, sojojin sun karanta sanarwar ƙwace mulkin ƙasar a hedikwatar rundunar da ke babban birnin ƙasar, Bissau.
Cikakken rahoto na tafe…
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sace ɗalibai: Ba rufe makarantu ba ne mafita — PDP
Jam’iyyar PDP ta yi soki matakin rufe makarantu da Gwamnatin Tarayya da wasu jihohi suka ɗauka sakamakon yawaitar sace-sacen dalibai, tana mai gargaɗin cewa hakan na iya taimaka wa ’yan ta’adda cimma burinsu.
A taron manema labarai da aka gudanar a Abuja a ranar Lahadi, kakakin jam’iyyar, Ini Ememobong, ya ce, ya buƙaci Shugaba Tinubu da ya ajiye muƙaminsa idan ba zai iya kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya.
“Muna sake tunatar da Shugaba Tinubu da gwamnatin APC cewa tsaron rayuka da dukiyoyi shi ne aikin farko na kowace gwamnati. Duk lokacin da gwamnati ta kasa yin wannan aiki, dole ta nemi taimako—na cikin gida ko na waje—ko kuma ta yi murabus idan tana da gaskiya da shugabanci,” in ji Ememobong
Ya ci gaba da cewa, “Idan aka rufe makarantu, to ’yan ta’adda sun cimma nasara.”
Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADCYa buƙaci gwamnati ta samar da tsari na musamman don magance matsalar tsaro, maimakon sauƙaƙa ta, ta hanyar rufe makarantu don kauce wa sace-sace da kuma neman yabo saboda siyasa.
Ememobong ya jaddada muhimmancin aiwatar da shirin samar da tsaro a makarantu, wanda ya ce ya ta’allaƙa ne kan bayanan sirri daga al’umma da kuma tsarin ɗaukar matakan gaggawa na dakile hare-hare.
Ya bayyana cewa rashin tsaro ya zama babban cikas ga ilimi a Najeriya, musamman a Arewacin ƙasar. Ya yi nuni da alƙaluman Asusun Kula da Ƙananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) da ke nuna cewa Arewacin Najeriya na da mafi yawan yara da ba sa zuwa makaranta—miliyan 10.2 a matakin firamare da miliyan 8.1 a sakandare.
Ememobong ya ce, “Wannan bayanin ba wai kawai yana nuna mummunan hoto ba, har ma yana bayyana ainihin halin da ake ciki a Najeriya. Jerin hare-hare da sace-sace a jihohi daban-daban cikin mako guda na nuna yadda rashin tsaro ya zama sabon yanayin rayuwa a ƙarƙashin gwamnatin APC ta Bola Tinubu.”
Ya kuma soki yadda gwamnati ke mayar da martani ga sace-sacen ɗalibai, yana mai cewa, “Abin damuwa shi ne, duk lokacin da irin wannan mummunan lamari ya faru, martanin gwamnati ba ya da ƙarfi kuma ba ya nuna tausayi.
“Misali, maimakon Shugaban Ƙasa ya ziyarci jihohin Kebbi da Neja don jajanta wa iyayen da ’ya’yansu ke hannun ’yan bindiga da kuma karfafa jami’an tsaro, sai kawai ya umarci Ƙaramin Ministan Tsaro ya koma Kebbi.”
Ya ƙara da cewa kwatanta yadda aka tura tawagPDP ta buƙaci Shugaba Tinubu da ya ajiye muƙaminsa idan ba zai iya kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya.a zuwa Majalisar Dokokin Amurka da taron G-20 da kuma yadda aka tura wakili guda zuwa Kebbi, ya nuna yadda Fadar Shugaban Ƙasa ke ɗaukar wannan matsala da sakaci.”
PDP ta sake jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa shi ne babban aikin kowace gwamnati.