Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar
Published: 23rd, November 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kebbi ta umarci rufe dukkan makarantun sakandare na gwamnati da na kuɗi tare da dukkan manyan makarantun gaba da sakandare a faɗin jihar.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da Kwamishinan Ilimi na Gaba da Sakandare Alhaji Issa Abubakar-Tunga da Kwamishinar Ilimi ta Firamare da Sakandare, Dakta Halima Bande, a Birnin Kebbi.
Kwamishinonin sun bayyana cewa rufe makarantun gwamnati da na kuɗi a jiha ya zama dole sakamakon hare-haren da aka kai a wasu sassan jihar kwanan nan.
Sun lissafa makarantun gaba da sakandare da abin ya shafa kamar haka:
Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kebbi da ke Dakingari da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Abdullahi Fodio da ke Aliero da Kwalejin Kimiyyar Lafiya da Fasaha ta Jega da Kwalejin Ilimi ta Adamu Augie da ke Argungu da Makarantar Sharar Fagen Shiga Jami’a ta Yauri.
Sai dai sun ce makarantar da kawai ba ta cikin jerin waɗanda aka rufe ita ce Kwalejin Kiwon Lafiya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar.
Yayin da suke kira ga dukkan shugabannin makarantun da su bi umarnin gwamnati, kwamishinonin sun shawarce su da su kasance cikin natsuwa domin za a sanar da sabuwar ranar koma makarantun nan gaba.
Sani Haruna Dutsinma
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnati Makarantu Umarni
এছাড়াও পড়ুন:
An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro
Hukumar Ilimi ta Matakin Farko ta Jihar Filato (PSUBEB) ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandire na gwamnati a faɗin jihar sakamakon fargabar tsaro da ta taso a kwanakin nan.
A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce za a rufe ƙananan makarantun sakandare tun daga Asabar, 22 ga Nuwamba, 2025, yayin da makarantun firamare za a rufe su daga Litinin, 24 ga Nuwamba, 2025.
H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jiharWannan mataki na zuwa ne bayan sace ɗalibai a wasu makarantu da ke jihohin Kebbi da Neja a ‘yan kwanakin da suka gabata, abin da ya tayar da hankalin iyaye da hukumomi.
PSUBEB ta sanar da cewa rufe makarantun mataki ne na wucin-gadi domin daƙile duk wata barazana da ka iya tasowa, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na ɗaukar lafiya da tsaron ɗalibai da muhimmanci.
Hukumar ta buƙaci Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi, shugabannin makarantu da shugabannin al’umma da su ba da cikakken haɗin kai wajen aiwatar da umarnin, tare da zama masu kula da duk wata alama ta rashin tsaro a yankunansu.