’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara
Published: 25th, November 2025 GMT
’Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 11, ciki har da wat mai juna biyu da ƙananan yara Jihar Kwara.
Maharan sun kai farmaki tare da sace mutanen ne a yankin Eruku da ke Ƙaramar Hukumar Ekiti da ke jihar.
Ƙarin bayani na tafe…
.উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga garkuwam sace mutane
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, ta daƙile wani hari da ’yan bindiga suka kai wa al’ummar Kuraje da ke gefen birnin Gusau.
Wasu gungun ’yan bindiga, ɗauke da makamai ne, suka kutsa cikin ƙauyen suna harbi, lamarin da ya jefa mazauna Kuraje da maƙotan ƙauyukan cikin tashin hankali.
Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta NejaA yayin harin, sun yi awon gaba da mata 10 da yara 15.
Kakakin rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya ce ’yan sanda sun ɗauki mataki bayan samun kiran gaggawa.
Ya ce tawagar haɗin gwiwa daga sashen Damba, Sashen Ayyuka da kuma Rundunar Tsaron Al’umma (CPG) sun isa ƙauyen cikin gaggawa.
Sun bi sahun ’yan bindigar, sannan suka yi artabu da su.
’Yan sanda sun ceto dukkanin mutum 25 ba tare da kowa ya ji rauni ba.
An kai matan da yaran zuwa Sabon Gari Damba domin kula da su, kafin su da iyalansu.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya yaba wa jarumtar jami’an da suka yi aikin, tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyinsu.