’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa
Published: 25th, November 2025 GMT
’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.
Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.
Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.
Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.
Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke FuskantaA cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.
Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.
Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.
Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Afuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar tsaro a Arewa na damuna matuƙa — Tinubu
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce matsalar tsaro a yankin Arewa na damunsa matuƙa saboda tana kawo cikas ga zaman lafiya da ci gaban Najeriya.
Ya bayyana haka ne a Jihar Kaduna, yayin bikin cikar Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), wanda Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas Tajudeen, ya wakilce shi.
’Yan sanda sun daƙile harin ’yan bindiga, sun ceto mutum 25 a Zamfara Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin NajeriyaTinubu, ya ce gwamnatinsa ta gaji matsalolin tsaro masu yawan gaske, amma tana aiki tuƙuru don magance su.
Ya yi gargaɗin cewa Najeriya ba za ta ci gaba ba idan al’ummarta suka ci gaba da fuskantar hare-hare, talauci, da tsoro.
“Ba abin da ke damuna kamar matsalar tsaro a Najeriya, musamman a Arewa. Ba za mu ci gaba ba idan wani yanki yana cikin matsala.”
Ya yi kira ga shugabannin Arewa da su zama masu gaskiya da jarumta wajen nemo mafita.
Ya kuma yi alƙawarin cewa gwamnatinsa za ta kawo ƙarshen ’yan ta’adda da ’yan fashi, tare da farfaɗo da tattalin arziƙin yankin.
“Mun gaza daga ranar da muka yi bacci lafiya alhali miliyoyin jama’a suna kwana cikin yunwa, matafiya suna tsoron yin tafiya.”
Tinubu ya ce yana fatan ganin Arewa mai aminci, ciki har da samar da man fetur daga yankunan Arewa da manyan ayyuka kamar sabon titin Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano.
Shugaban kwamitin amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu, ya yi Allah-wadai da kashe-kashe da garkuwa da ɗalibai da malamai a jihohin Neja da Kebbi.
Ya roƙi gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa don kawo ƙarshen tashin hankali.
“Kashe-kashe, sace ɗalibai, da hare-haren da ake kai wa jami’an tsaro ba za su ci gaba da aukuwa ba. Gwamnati dole ta nemo hanyar kawo ƙarshen wannan lamari.”