An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
Published: 28th, November 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Anambra ta gano gawar wasu mata uku ’yan ƙasar Kamaru da ake zargin waɗanda suka yi garkuwa da su domin neman kuɗin fansa sun kashe su.
Haka kuma, rundunar ta ce ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a lamarin, Nonso Augustine Akpeh da Kingsley Akpeh, waɗanda ake zargin suna cikin gungun masu garkuwar da suka sace matan.
Tun dai a ranar Litinin, 10 ga watan Nuwamban nan ne aka sace matan a garin Anam da ke Jihar Anambra, inda suka saba zuwa sayen kayayyakin kasuwanci.
Jami’an rundunar na sashen yaki da masu garkuwa da mutane da ke Awkuzu ne suka kai wani farmaki, inda aka yi musayar wuta tsakaninsu da masu garkuwar.
A yayin bincike, an gano makamai iri-iri, ciki har da bindiga mai sarrafa kanta da bindigogi ƙirar hannu da kuma harsasai.
Kakakin rundunar, SP Tochukwu Ikenga, ya shaida wa Aminiya cewa dangin matan ne suka kai rahoton bacewar su tun a ranar 13 ga Nuwamba, bayan sun gaza komawa gida daga kasuwar Anam, inda suka saba zuwa.
SP Ikenga ya ce masu garkuwa sun fara neman kuɗin fansa har Naira miliyan 50, amma bayan an yi ciniki suka amince a biya Naira miliyan 2.9.
Sai dai a cewar SP Ikenga, masu garkuwar sun kashe matan duk da ’yan uwan waɗanda abin ya shafa sun biya kuɗin fansar.
A cewar SP Ikenga, wani cikin waɗanda ake zargin ne ya jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa dajin da ake ɓoye waɗanda aka sace, inda a can ne aka gano wurin da ake jefar da gawawwakin nasu.
A yayin binciken ne ɗaya daga cikin ababen zargin ya yi yunƙurin tserewa, amma jami’an suka sake cafke shi.
Mazauna yankin da ke kusa da dajin sun tabbatar wa ’yan sanda cewa wurin ya shahara wajen jefar da gawar mutanen da masu garkuwa da mutane ke kashewa.
Rundunar ’yan sandan ta ce bincike zai ci gaba da gudana, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane jihar Anambra da ake zargin masu garkuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
An sake tabbatar wa ma’aikatan Gwamnatin Tarayya FG da suka yi ritaya cewa za a biya su wani bangare na kudaden ariyas a cikin wannan watan, kamar yadda hukumomin da abin ya shafa suka yi alkawari.
Mataimakin Sakataren ƙungiyar masu karɓar fansho ta ƙasa, Alhaji Ahmed Gazali, ya bayar da wannan tabbaci yayin da ake tattaunawa da shi ta wayar tarho daga Abuja.
Alh. Ahmed Gazali, ya yi bayanin cewas daraktan dake kula da kudade na ofishin akanta janar na tarayya ya tabbatar da daukan matakin hakan na biyan kudaden.
Ya bayyana fatan ganin kudirin FG na gaggauta biyan kudade, domin dakatar da duk wata zanga zanga wanda hakan bai dace ba ga ma’aikatan da suka yi ritaya domin bata martaban kasan nan.
Hakan kuma masu karban fensho a Radion Tarayya na kasa FRCN da Gidan talabijin na kasa NTA dake Kaduna sun nuna damuwarsu game da zargin da ake yi cewa ana kokarin wulakanta shugabannin kungiyar ma’aikatan da suka yi ritaya karkashin jagorancin kwamaret Munkaila Ogunbote.
DAGA SULEIMAN KAURA