ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin November 15, 2025 Daga Birnin Sin Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya November 14, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba November 14, 2025

.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan

Wasu Yahudawa ’yan kama-wuri-zauna sun lalata tare da kona wani masallaci da ke gabar yammacin kogin Jodan da Isra’ila ta mamaye, kamar yadda kamfanin dillancin Labarai na Falasɗinu (WAFA) ya ruwaito a ranar Alhamis.

WAFA ya ce Yahudawan sun kuma yi rubuce-rubucen batanci a bangon masallacin da ke cikin wani ƙauye a arewa maso yammacin yankin, da safiyar ranar.

HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani

Wasu kafafen yaɗa labarai kuma sun ce rubuce-rubucen da aka fesa da fenti sun haɗa da cin mutuncin Annabi Muhammad (SAW) da harshen Ibrananci.

Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana gudanar da bincike kan zargin.

Babu rahoton rauni ko mutuwa a lamarin kawo yanzu, amma bidiyon da ke yawo a kafafen yada labaran Falasɗinu da Isra’ila sun nuna lalacewar masallacin.

Shugaban Isra’ila, Isaac Herzog, ya bayyana harin a matsayin “mai matuƙar daure kai.”

Herzog ya ce wannan laifin da “ƙalilan daga cikin masu laifi” suka aikata ya “saba ka’ida,” inda ya ƙara da cewa “dukkan hukumomin gwamnati dole su ɗauki mataki mai ƙarfi don kawar da wannan dabi’a.”

Babban hafsan sojin Isra’ila, Laftanar Janar Eyal Zamir, ya goyi bayan suka da Herzog ya yi, yana mai cewa rundunar soji “ba za ta lamunci ayyukan wasu ’yan ƙalilan masu laifi da ke bata sunan jama’ar da ke bin doka ba.”

Sakataren Janar na Majalisar Dinkin Duniya (UN), Antonio Guterres, a ranar Alhamis, ya la’anci harin da Yahudawan masu haramtattun gidajen suka kai kan masallaci a yankin wanda Isra’ila ta mamaye.

Tashin hankali daga Yahudawa masu ra’ayin rikau kan Falasɗinawa a yankin ya ƙaru tun bayan fara yaƙin Gaza a watan Oktoban 2023, wanda aka fara bayan hare-haren da Hamas ta jagoranta kan Isra’ila.

Tun daga lokacin, an samu ƙaruwar hare-haren da ke haddasa mutuwa tsakanin Falasɗinawa da sojojin Isra’ila a yankin na Yammacin Kogin na Jodan.

Rundunar sojin Isra’ila na yawan fuskantar zargi kan gazawarta wajen ɗaukar mataki mai ƙarfi kan tashin hankalin da Yahudawa ke haddasawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin
  • Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba
  •  Amurka Ta Sanar Da Fara Kai Farmakin Soja Mai Sunan ” Mashin Kudu” Akan Yankin Latin
  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan
  • Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki