Atiku ya karyata ba sojan da ya yi takaddama da Wike kyautar motar SUV
Published: 13th, November 2025 GMT
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya karyata rahotannin da ke cewa ya bai wa Laftanar Ahmed Yerima, sojan ruwan nan da ya samu takaddama da Ministan Abuja, Nyesom Wike, kyautar sabuwar mota kirar Toyota SUV.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar ta shafinsa na X a ranar Alhamis, Atiku ya bayyana labarin da ke yawo a kafafen sada zumunta a matsayin ƙarya tsagwaronta ba tare da wata hujja ba.
Ibe ya bukaci jama’a da su yi watsi da wannan labari da aka ƙirƙira.
“Mai girma Atiku Abubakar, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Najeriya (1999–2007), bai bai wa Laftanar Ahmed Yerima, ko wani mutum ba, sabuwar motar Toyota SUV, sabanin rahotannin ƙarya da ke yawo a kafafen sada zumunta.
“Labarin ƙarya ne gaba ɗaya kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi,” in ji shi.
Zargin da ya fara yawo a Facebook a ranar Laraba ya ce Atiku ya ba da kyautar motar ga sojan ruwa bayan takaddamar da ya samu da Wike kan wani rikicin fili a Abuja.
Takaddamar ta faru ne a ranar Talata lokacin da Wike ya yi arangama da sojan ruwan yayin da yake duba wani fili da ake takaddama a kan shi a unguwar Gaduwa da ke cikin Babban Birnin Tarayya.
Bidiyon lamarin da ya yadu a intanet ya nuna yadda aka yi musaya yawu mai zafi tsakanin ministan da sojan.
Lamarin ya haifar da ce-ce-ku-ce a fadin ƙasa, inda fitattun mutane da dama, ciki har da tsohon Shugaban Rundunar Sojin Ƙasa, Janar Tukur Buratai (mai ritaya), da wasu ’yan siyasa, suka bukaci a kai zuciya nesa kuma a girmama dokokin kasa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
Ya ce, wanda ake kara ya nema kuma an bashi kudin fansa har Naira miliyan 15 daga iyalan wanda aka kashe kafin su kashe shi.
“Sun bugi wanda aka kashe a kai da ƙirji da sanda sannan daga baya suka binne gawar a gidan Adamu da ke Dawakin Kudu,” in ji mai gabatar da kara ga kotun.
Da take yanke hukunci, Mai Shari’a Aisha Mahmoud ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da hujjoji game da karar da suka shigar a kan Adamu ba tare da wata shakka ba.
“Ina yanke wa Adamu hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda ya buga wa wanda aka kashe sanda a kansa da ƙirjinsa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa. Ubangiji ya yi masa rahama,” in ji ta.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA