Aminiya:
2025-11-13@12:38:53 GMT

Atiku ya karyata ba sojan da ya yi takaddama da Wike kyautar motar SUV

Published: 13th, November 2025 GMT

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya karyata rahotannin da ke cewa ya bai wa Laftanar Ahmed Yerima, sojan ruwan nan da ya samu takaddama da Ministan Abuja, Nyesom Wike, kyautar sabuwar mota kirar Toyota SUV.

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya fitar ta shafinsa na X a ranar Alhamis, Atiku ya bayyana labarin da ke yawo a kafafen sada zumunta a matsayin ƙarya tsagwaronta ba tare da wata hujja ba.

An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe Gwamnatin Tarayya ta dakatar da harajin kashi 15 na shigo da fetur da dizal

Ibe ya bukaci jama’a da su yi watsi da wannan labari da aka ƙirƙira.

“Mai girma Atiku Abubakar, Mataimakin Shugaban Ƙasa na Najeriya (1999–2007), bai bai wa Laftanar Ahmed Yerima, ko wani mutum ba, sabuwar motar Toyota SUV, sabanin rahotannin ƙarya da ke yawo a kafafen sada zumunta.

“Labarin ƙarya ne gaba ɗaya kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi,” in ji shi.

Zargin da ya fara yawo a Facebook a ranar Laraba ya ce Atiku ya ba da kyautar motar ga sojan ruwa bayan takaddamar da ya samu da Wike kan wani rikicin fili a Abuja.

Takaddamar ta faru ne a ranar Talata lokacin da Wike ya yi arangama da sojan ruwan yayin da yake duba wani fili da ake takaddama a kan shi a unguwar Gaduwa da ke cikin Babban Birnin Tarayya.

Bidiyon lamarin da ya yadu a intanet ya nuna yadda aka yi musaya yawu mai zafi tsakanin ministan da sojan.

Lamarin ya haifar da ce-ce-ku-ce a fadin ƙasa, inda fitattun mutane da dama, ciki har da tsohon Shugaban Rundunar Sojin Ƙasa, Janar Tukur Buratai (mai ritaya), da wasu ’yan siyasa, suka bukaci a kai zuciya nesa kuma a girmama dokokin kasa.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata

Wani mutum da ba a gano sunansa ba ya mutu bayan da ya shiga wani gidan karuwai domin ganawa da ’yan mata masu zaman kansu a birnin Fatakwal.

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, inda rahotanni suka ce mamacin ya shiga gidan karuwai ne domin yin hulɗa da ’yan mata, sai dai ba a tabbatar da abin da ya jawo mutuwarsa ba.

Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin, inda ta ce an miƙa batun zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Jihar (SCID) domin gudanar da cikakken bincike.

Wasu majiyoyi daga cikin gidan karuwan sun bayyana cewa wani ma’aikacin otal ɗin da ke kula da wurin ya yi faɗa da mamacin kafin daga bisani ya yanke jiki ya faɗi ya mutu.

Matar tsohon Shugaban Ƙasa Shagari ta rasu EFCC na neman tsohon Gwamnan Bayelsa ruwa a jallo

Majiyar ta ƙara da cewa an garzaya da mutumin asibiti domin ba shi agajin gaggawa, amma daga bisani likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.

Rahotanni sun ce an kama wani mutum daga cikin gidan matan da ake zargi da hannu a lamarin, kuma rundunar ’yan sanda ta jihar ta ta fara bincike a kai.

SP Grace Iringe-Koko ta kuma tabbatar da cewa an kama mutum ɗaya da ake zargi, kuma sashen ’yan sanda na Azikiwe ya miƙa shari’ar zuwa SCID domin gudanar da bincike mai zurfi.

Sai dai bayan faruwar lamarin, an lura dukkan ’yan mata masu zaman kansu da ke yawo a cikin da wajen gidan karuwan sun yi layar zana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Atiku ya musanta labarin ba sojan da ya yi takaddama da Wike kyautar motar SUV
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
  • An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano
  • Wike: Za mu kare duk wani soja da ke aiki bisa doka — Ministan Tsaro
  • An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano
  • Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
  • Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu
  • Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata
  • Matar tsohon Shugaban Ƙasa Shagari ta rasu