Aminiya:
2025-11-14@22:40:07 GMT

Gwamnati na jefa makomar ilimi cikin hatsari — ASUU

Published: 15th, November 2025 GMT

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU), reshen Nsukka ta ce Gwamnatin Tarayya na lalata makomar ƙasar nan saboda rashin cika yarjejeniyar 2009.

A taron manema labarai da ta gudanar a Jami’ar Jihar Benuwe da ke Makurdi, Kodinatan yankin, Kwamared Christian Opata, ya ce gwamnati ba ta jajirce wajen magance matsalolin da suka shafi ɓangaren ilimi.

Ya yi magana ne a madadin jami’o’i takwas da ke yankin.

Opata, ya ce an tattauna tare da ƙumla yarjejeniyoyi da dama tsakanin ASUU da gwamnati tsawon shekaru, amma babu wani ci gaba da aka samu.

Ya zargi jami’an gwamnati da yin lƙawarin ƙarya da gangan.

Ya ce ASUU ta dakatar da yajin gargaɗin da ta yi kwanan nan saboda ɗalibai, iyaye, da ƙungiyoyin ƙwadago, amma har yanzu gwamnati ba ta ɗauki aniyar warware matsalar ba.

Opata, ya gargaɗi gwamnati cewa idan ba ta kammala tattaunawar cikin wata ɗaya ba, jami’o’i na iya sake tsunduma yajin aiki.

ASUU, ta kuma zargi wasu jami’an gwamnati da yaɗa bayanan ƙarya game da tattaunawar, musamman batun biyan bashin albashi da wasu kuɗaɗen da aka riƙe musu.

Kungiyar ta ce Najeriya na da isasshen kuɗi, amma gwamnati ce ba ta yi niyyar saka hannun jari a ilimi.

Sun roƙi sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin ƙwadago, ɗalibai, da ƙungiyoyi masu zaman kansu da su matsa wa gwamnati lamba don ganin an daidaita abubuwa.

ASUU ta ce malamai na cikin tsaka mai wuya saboda ƙarancin albashi, kuma ba ya isarsu wajen al’amuransu na yau da kullum.

Ƙungiyar ta sake jaddada cewa lokaci ya yi da gwamnati za ta cika alƙawarun da ta ɗauka a baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Alƙawari Ɗalibai tattaunawa Yajin aiki yarjejeniya

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Laraba, Sakataren Yada Labarai na ofishin mataimakin gwamna, Ibrahim Shu’aibu, ya bayyana lamarin a matsayin “cin amana a fili da direban da aka kama ya yi.”

 

“Ofishin Mataimakin Gwamna ya yaba wa binciken gaggawa da rundunar tsaron ta yi ta hanyar amfani da kaifin basira da kwarewa,” in ji sanarwar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro November 12, 2025 Manyan Labarai Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa November 12, 2025 Manyan Labarai Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna November 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai ta dage lokacin fara yin jarabawar WAEC a kwamfuta zuwa 2030
  • Ina girmama sojojin Nijeriya — Wike
  • NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane
  • Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25
  • Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
  • An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Kano Ta Kaddamar da Kwamitin Jagoranci Don Shirin Tarayyar Turai na Ilimi da Ƙarfafa Matasa
  • Hukumar Tsara Birane ta Kano Ta Fara Horar da Ma’aikata Kan Dokokin Aiki