Kyaftin ɗin tawagar ƴan wasa matan Nijeriya ƴan ƙasa da shekara 17 (Flamingos), Shakirat Moshood, na cikin jerin ƴan wasa uku da suka kai matakin ƙarshe domin lashe ƙyautar Matashiyar Ƴar Wasan CAF ta 2025. Sauran ƴan wasan da ke fafatawa da ita su ne Moha El Madani daga Morocco da Adji Ndiye ta Senegal.

Moshood ta yi fice a manyan wasanninta a gasar cin kofin Duniya na mata ƴan ƙasa da shekara 17 ta FIFA a 2025, ko da yake tawagar da Bankole Olowookere ke jagoranta ta tsaya a zagaye na 16. A duk tsawon gasar, ta kasance ɗaya daga cikin fitattun ƴan wasan da suka yi ƙwazo a tawagar da kyakkyawan salon wasa.

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Shakirat, wadda ke taka leda a Bayelsa Queens, ta kuma haskaka a gasar Premier ta mata ta Nijeriya (NWFL), inda ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar wa ƙungiyar nasarar lashe kofin a watan Mayu. Haka kuma ta kasance cikin manyan ƴan wasan da suka zura ƙwallo a wasan neman shiga gasar zakarun mata ta WAFU B a ƙasar Cote d’Ivoire.

ADVERTISEMENT

Zaɓenta cikin jerin ƴan wasa uku na ƙarshe ya ƙara tabbatar da tasirinta a ƙwallon ƙafa, tare da mayar da ita daya daga cikin fitattun matasan ƴan wasa da ke tasowa a nahiyar Afrika.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe November 14, 2025 Wasanni Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati November 14, 2025 Manyan Labarai Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4 November 13, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kwanan baya, firayim ministan Japan Takaichi Sanae ta yi ikirari a fili cewa, “lamarin Taiwan lamari ne na Japan”, kuma tana da alaka da aiwatar da ikon kare kai na gama kai, inda a karon farko hakan ya nuna tsoma baki cikin batun Taiwan ta hanyar amfani da makamai, kuma a karon farko ya yi barazanar yin amfani da karfin tuwo kan kasar Sin.

Kalaman Takaichi game da Taiwan sun tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma sun saba wa dokokin kasa da kasa da ka’idojin asali na dangantakar kasa da kasa, da lalata tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu, kana sun saba wa ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” da ruhin takardu hudu na siyasa tsakanin Sin da Japan, kazalika sun lalata tushen siyasa na dangantakar Sin da Japan, kuma sun cutar da jama’ar Sin.

Ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” ta samu amincewa a tsakanin daukacin al’ummun duniya. Taiwan wani yanki na Sin da ba za a iya ware shi ba, kuma al’amuran Taiwan cikakkun al’amuran cikin gida ne na Sin, sannan wannan gaskiya ce da duniya ta amince da ita, kuma wani muhimmin bangare ne na tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu.

ADVERTISEMENT

Kalubalantar ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” tamkar wasa da wuta ne, kuma tabbas kaikayi zai koma kan mashekiya, don haka ya kamata Japan ta yi waiwaye a kan tarihi, ta janye kalaman da ba su dace ba! (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan  November 13, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia November 13, 2025 Daga Birnin Sin Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana November 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
  • Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
  • Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
  • Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Nijeriya za ta kece raini da Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • ‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026
  • Super Falconets ta lashe gasar WAFU ta ’yan ƙasa da shekaru 20
  • Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — Ronaldo