Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
Published: 14th, November 2025 GMT
Kwanan baya, firayim ministan Japan Takaichi Sanae ta yi ikirari a fili cewa, “lamarin Taiwan lamari ne na Japan”, kuma tana da alaka da aiwatar da ikon kare kai na gama kai, inda a karon farko hakan ya nuna tsoma baki cikin batun Taiwan ta hanyar amfani da makamai, kuma a karon farko ya yi barazanar yin amfani da karfin tuwo kan kasar Sin.
Kalaman Takaichi game da Taiwan sun tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma sun saba wa dokokin kasa da kasa da ka’idojin asali na dangantakar kasa da kasa, da lalata tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu, kana sun saba wa ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” da ruhin takardu hudu na siyasa tsakanin Sin da Japan, kazalika sun lalata tushen siyasa na dangantakar Sin da Japan, kuma sun cutar da jama’ar Sin.
Ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” ta samu amincewa a tsakanin daukacin al’ummun duniya. Taiwan wani yanki na Sin da ba za a iya ware shi ba, kuma al’amuran Taiwan cikakkun al’amuran cikin gida ne na Sin, sannan wannan gaskiya ce da duniya ta amince da ita, kuma wani muhimmin bangare ne na tsarin kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu.
ADVERTISEMENTKalubalantar ka’idar “kasar Sin daya tak a duniya” tamkar wasa da wuta ne, kuma tabbas kaikayi zai koma kan mashekiya, don haka ya kamata Japan ta yi waiwaye a kan tarihi, ta janye kalaman da ba su dace ba! (Mai zane da rubutu: MINA)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
Hukumar zaben kasar Habasha ta sanar da cewa za a yi manyan zabukan kasar a ranar 1 ga watan Yuni na 2026.
Shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha Melatwork Hailu ta fada wa kafafen watsa labarun kasar cewa; Ana gudanar da ayyukan ne a yanzu domin tsara wuraren da za a yi zabukan da samar da rumfunan zabe a cikin rassan da za a kada kuri’a.”
Har ila yau shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha ta ce, jam’iyyun siyasar kasar sun sami horon da ya dace domin bayyana da tallata manufofinsu ga jama’ar kasar.
Sai dai yin zabe a kasar ta Habasha yana fuskantar kalubale mai yawa. Kasar dai ba ta dade da fitowa daga yakin basasa ba wanda aka yi a tsakanin gwamnatin tarayya da yankin Tigray da aka yi a tsakanin 2020 zuwa 2022.
Rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 600,000, kuma wasu da adadinsu ya kai miliyan 1 su ka bar gidajensu.
Kuma har yanzu ana fama da tashe-tashen hankula a cikin yankunan Oromia da Amhara.
A jawabin da ya gabatar a ranar 28 ga watan Oktoba, Fira ministan kasar ta Habasha Abiy Ahmed ya ce; Gwamnatin kasar tana da karfin da za ta iya gudanar da zabukan.”
Haka nan kuma ya ce, zaben da za a yi zai zama shi ne mafi tsaruwa a tarihin kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci