Aminiya:
2025-11-27@20:43:13 GMT

El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC

Published: 27th, November 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya sauka sheƙa daga jam’iyyar SDP zuwa jami’yyar haɗaka ta ADC.

Komawar El-Rufai jam’iyyar ADC a hukumance wani mataki ne da ake ganin zai kawo sabon salo a siyasar adawa wajen ƙalubalantar jam’iyyar APC mai mulki a Zaɓen 2027.

An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos

A wannan Alhamis ɗin ce El-Rufai ya kammala rajistar zama mamba na jam’iyyar ADC a mazaɓarsa ta Unguwar Sarki da ke birnin Kaduna, inda ya yi alƙawarin amfani da jam’iyyar ADC wajen fuskantar abin da ya kira rashin ƙwarewa a jagorancin gwamnatin jihar.

“Ina da cikakkiyar rajista a jam’iyyar African Democratic Congress,” in ji shi a gaban manyan jami’an jam’iyyar, ciki har da Mataimakin Shugaban ADC na Arewa maso Yamma, Jafaru Sani, da Sakataren Yi wa Mambobi Rajistar Jam’iyyar na Ƙasa, Sanata Sadiq Yar’adua.

A watan Maris na bana ne dai El-Rufai ya sauya sheƙa daga APC zuwa SDP a wani yunƙuri na shirya haɗin gwiwar adawa, sai dai ya ce tattaunawar da suke yi a SDP ɗin ta gaza haifar da ɗa mai ido wajen cimma muradinsu saboda “tsoma bakin gwamnati da kuma cin hanci da wasu shugabannin jam’iyyar ke yi.”

Da yake jawabi kan siyasar Jihar Kaduna, El-Rufai ya yi kira ga jama’a da su yi rajista da ADC domin “maimaita abin da muka yi a 2015,” yana mai zargin gwamnatin APC mai ci da sakaci da jagorancin al’umma.

“Ina kira ga dukkan ’yan Kaduna masu shekaru 18 zuwa sama da su fito su yi rajista. Da ikon Allah, zamu sake kawar da gwamnatin da ta nuna gazawa.

“Mu da muka taimaka muka ɗora su a kujerar mulki, za mu taimaka wajen dawo da su gida… kafin su wuce kotu,” in ji El-Rufai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: El Rufai ya a jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Bauchi, a matsayin babban rashi ga al’umma.

Gwamnan ya bayyana malamin a matsayin jagoran haɗin kai, zaman lafiya, da fahimtar juna tsakanin Musulmi da mabiya addinai daban-daban.

’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa

A cikin saƙon ta’aziyya da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Gidado, ya sanya wa hannu, gwamnan ya ce Gwamnatin Jihar Bauchi tana alhinin rasuwar malamin.

Dahiru Bauchi, ya rasu da safiyar ranar Alhamis, 27 ga watan Nuwamba, 2025 a Bauchi, yana da shekara 102.

Gwamnan, ya ce Sheikh Dahiru Bauchi babban malami ne na addinin Musulunci, mai imani, tawali’u da hikima.

A cewarsa ya sadaukar da rayuwarsa wajen yaɗa addinin Musulunci, koyar da Alƙur’ani, da kuma taimaka wa mutane wajen tarbiyya.

Marigayin, ya koyar da dubban ɗalibai da suka haddace Alƙur’ani tare da yaɗa addinin Musulunci a sassan nahiyar Afrika.

Gwamnan, ya ƙara da cewa gudunmawar da marigayin ya bayar a fannin tafsiri, fiqhu da tarihi sun taka muhimmiyar rawa wajen ɗora al’umma kan turbar tsira.

Har ila yau, ya ce Gwamnatin Jihar Bauchi za ta ci gaba da girmama marigayin ta hanyar tallafa wa makarantu da manufofin da ya gina, musamman a fannin ilimin addinin Musulunci, tarbiyya da ci gaban al’umma.

Ya yi addu’a rAllah ya gafarta masa kurakuransa, ya sanya shi aAljannatul Firdausi, ya kuma bai wa iyalansa, mabiyansa da ɗaukacin al’ummar Musulmi haƙurin rashinsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Bauchi ya yi ta’aziyyar rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Allah Ya yi wa Sheikh Dahiru Bauchi rasuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Harkar Tsaro Tare da Bada Umurnin Daukar Sabbin Jami’ai
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina