Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-25@22:19:41 GMT

Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa

Published: 26th, November 2025 GMT

Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya gabatar da kasafin kuɗi na shekarar 2026 na sama da naira biliyan 900 ga Majalisar Dokokin jihar.

Yayin gabatar da kasafin da aka lakaba wa suna Kasafin Kirkire-kirkire da Sauyi Don Cigaban Jigawa II,” Gwamna Namadi ya ce za a ware sama da naira biliyan 693.

4, wanda ya kai kimanin kashi 76 cikin 100, don ayyukan raya kasa.

Gwamnan ya kuma ce sama da naira biliyan 208 za su tafi ne ga ayyukan yau da kullum.

A cewarsa, an ware sama da naira biliyan 310 ga bangaren ilimi da lafiya, yayin da kimanin naira biliyan 186 za su tafi ga hanyoyi da sufuri.

Malam Umar Namadi ya ƙara da bayyana cewa an ware sama da naira biliyan 74 ga bangaren noma da kiwo, sai naira biliyan 50.74 don wutar lantarki da makamashi, yayin da naira biliyan 12.68 za su tafi ga shirin ƙarfafa matasa.

Ya nuna cewa an tanadi naira biliyan 25.4 don ruwa da tsafta, sannan naira biliyan 35.4 don muhalli da sauyin yanayi.

Gwamna Namadi ya kuma gabatar da sama da naira biliyan 288 don ayyukan kananan hukumomi 27 na jihar.

 

Radio Nigeria ya ruwaito cewa kasafin shekarar 2026 ya fi na shekarar 2025 da kaso 19 cikin 100.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa sama da naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro

Hukumar Ilimi ta Matakin Farko ta Jihar Filato (PSUBEB) ta bayar da umarnin rufe dukkan makarantun firamare da sakandire na gwamnati a faɗin jihar sakamakon fargabar tsaro da ta taso a kwanakin nan.

A sanarwar da hukumar ta fitar, ta ce za a rufe ƙananan makarantun sakandare tun daga Asabar, 22 ga Nuwamba, 2025, yayin da makarantun firamare za a rufe su daga Litinin, 24 ga Nuwamba, 2025.

H-JRBDA ta yi alƙawarin magance ambaliyar ruwa a Jigawa Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar

Wannan mataki na zuwa ne bayan sace ɗalibai a wasu makarantu da ke jihohin Kebbi da Neja a ‘yan kwanakin da suka gabata, abin da ya tayar da hankalin iyaye da hukumomi.

PSUBEB ta sanar da cewa rufe makarantun mataki ne na wucin-gadi domin daƙile duk wata barazana da ka iya tasowa, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na ɗaukar lafiya da tsaron ɗalibai da muhimmanci.

Hukumar ta buƙaci Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi, shugabannin makarantu da shugabannin al’umma da su ba da cikakken haɗin kai wajen aiwatar da umarnin, tare da zama masu kula da duk wata alama ta rashin tsaro a yankunansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka
  • An rufe makarantun Filato saboda matsalar tsaro