2025-10-13@17:56:10 GMT
إجمالي نتائج البحث: 4206
«yan kasuwa a jihar»:
(اخبار جدید در صفحه یک)
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa kasar ta shiga sabon salo na gyaran tattalin arziki, kuma matsin da ake ciki na dab da wucewa su zama tarihi. A cikin jawabinsa ga ’yan kasa don bikin cikar Najeriya shekara 65 da samun ’yancin kai, shugaban ya ce gwamnatinsa ta damu da radadin da mutane ke ciki sakamakon gyare-gyaren da ake aiwatarwa. Sai dai ya jaddada cewa da Najeriya ba ta dauki matakan da ta dauka ba, da tuni ta shiga halin karyewar tattalin arziki. Yunwa na kashe ’yan Najeriya, amma Tinubu ko a jikinsa – Atiku DAGA LARABA: Tasirin Bambance-bambance Tsakanin ‘Yan Najeriya Shekara 65 Da Samun ‘Yancin Kai Tinubu ya tuna da jaruman da suka...
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya fada a jiya Talata cewa ya bayar da umarnin aikewa da jiragen ruwa masu ninkaya a karkashin ruwa dake dauke da makaman Nukiliya da su karaci gabar ruwan kasar Rasha, a matsayin kandagarko. Trump ya kara da cewa; A cikin kwanakin bayan an aiko mana sakon barazana daga Rasha, don haka na aike da jiragen ruwa masu makaman Nukiliya da shi ne makamai mafi hatsari.” Shugaban kasar na Amurka ya riya cewa kasarsa tana gaba da kasashen Rasha da China da ci gaban shekau 25 a fagagen kimiyya dakuma kera jiragen ruwa masu ninkaya a karkashin ruwa.” Share 0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my...
A yau Talata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun, ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum. Inda game da rahoton ci gaban Sin na 2025 da cibiyar nazarin samar da ci gaba ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta fitar, Guo ya ce ci gaban Sin mai inganci ya samar da damammaki ga duniya. Dangane da furucin Amurka na cewa za ta kara haraji kan katako, da kayan da ake sarrafawa daga gare shi, da ake shigarwa kasar daga ketare, Guo Jiakun ya bayyana cewa, ba za a samu nasara a yakin ciniki da yakin haraji ba, kuma babu wata hanya ta fita daga ra’ayin ba da kariya ga kasuwa. Game da shawarar da Amurka ta gabatar...
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya jinjina wa ’yan Najeriya bisa abin da ya kira “juriya, haƙuri da ƙarfin halin da suke nunawa duk da matsin tattalin arziki da matsalolin tsaro” da ƙasar ke fuskanta. A cikin saƙonsa na taya ’yan Nijeriya murnar zagayowar ranar samun ’yancin kai da ƙasar ta yi shekaru 65 da suka gabata, madugun adawar ya yi zargin cewa, gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki ta yi watsi da halin ƙaƙanikayi da ’yan ƙasar suka tsinci kansu a halin yanzu. A gaggauta binciko makasan ’yar jaridar Arise TV —Tinubu ’Yan sanda sun cafke ababen zargi 4 a Yobe Wazirin Adamawan ya bayyana damuwa kan yadda ’yan Najeriya ke rayuwa cikin ƙangin talauci, da yunwa, da rashin...
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira ga daukacin jama’ar kasar Sin da su yi aiki tukuru, tare da ingiza wanzar da zamanantarwa irin ta Sin. Xi, wanda kuma shi ne sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar zartarwar rundunar sojojin Sin, ya yi kiran ne yayin taron bikin cika shekaru 76 da kafuwar janhuriyar jama’ar kasar Sin, wanda ya gudana yau Talata a babban dakin taruwar jama’a dake birnin Beijing. Shugaba Xi, ya jaddada cewa a gabar da yanayin harkokin duniya ke saurin sauyawa cikin sama da karni guda, dole ne a yi aiki tukuru wajen yayata akidun bai daya na dukkanin bil’adama, da aiwatar da tsarin cudanyar mabanbantan sassa, da ingiza aiwatar da shawarwarin bunkasa ci gaban...
Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da uwargidansa, Sanata Oluremi Tinubu sun bayyana alhini kan kisan gillar da aka yi wa Somtochukwu ‘Sommie’ Maduagwu, waata ’yar jarida mai gabatar da labarai a gidan Talabijin na ARISE TV. A wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa ta fitar, shugaba Tinubu da uwargidansa sun yi Allah-wadai da kisan, suna mai bayyana cewa a matsayin babban rashi a ƙasar da kuma fagen aikin jarida. ’Yan sanda sun cafke ababen zargi 4 a Yobe An ƙaddamar da shirin rajistar yaran da ba su zuwa makaranta a Gombe Aminiya ta ruwaito cewa, marigayiyar ta rasu ne bayan wani farmaki da ’yan fashi suka kai gidanta da ke Katampe a Abuja, a ranar Litinin da ta gabata. Tinubu...
Sanarwar ta kara da cewa, “Wannan aiki daya tilo na karamci da adalci ya sake farfado da fatan ma’aikatan jinya da yawa a cikin gwamnatin ku da kuma a cikin ajandar sabunta fata na Shugaban kasa,” in ji sanarwar. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin soma karɓar haraji daga hannun mata masu zaman kansu waɗanda suka mayar da karuwanci sana’a. Shugaban kwamitin shugaban ƙasa kan manufofin kuɗi da gyaran dokokin haraji, Taiwo Oyedele, ya ce kuɗaɗen da masu sana’ar karuwanci ke samu za a riƙe cire musu haraji a ƙarƙashin sabuwar dokar haraji ta ƙasar. Oyedele ya yi wannan bayani ne a wani faifan bidiyo da ya wallafa a shafin X a jiya Litinin, inda ya kawo misalan hanyoyin samun kuɗin da ake sanya wa haraji. Masanin harajin ya bayyana cewa sabbin dokokin ba su bambanta tsakanin hanyar halal ko ta haram wajen samun kuɗi ba — abin da suke dubawa kawai shi ne ko kuɗin ya fito daga...
Fadar Gwamnatin Nijeriya ta sanar da cewa duk da tana maraba da tsayawa takarar tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan a Zaɓen 2027, amma ya kwana da sanin cewa har yanzu ’yan ƙasar ba su mance da badaƙalar da aka tafka a lokacin gwamnatinsa ba. Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ya fitar da yammacin ranar Litinin, ta ce ’yan Najeriya na sane da “rashin takaɓus” a mulkin Jonathan ɗin na shekarun baya. Jama’ar gari sun kama ’yan bindiga 3 a Kastina An yi garkuwa da tsohon Shugaban SUBEB na Jihar Neja Sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasar ta fitar mai taken “Muna maraba da tsohon shugaban ƙasa zuwa takarar shugabancin ƙasa”, “amma ’yan Najeriya na sane...
Tsohon Shugaban Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Neja (SUBEB), Alhaji Alhassan Bawa Niworo, ya shiga hannun ’yan bindiga. An yi garkuwa da shi tare da wasu fasinjoji da dama a yammacin Litinin, 29 ga Satumba, 2025, da misalin ƙarfe 4 na yamma, tsakanin ƙauyukan Felegi da Ibi a kan hanyar Mokwa zuwa New Bussa a Ƙaramar Hukumar Borgu. Wata majiya ta ce Niworo tare da wasu ciki har da wani lauya, Barista Ahmad, na kan hanyarsu zuwa Minna ne lokacin da ’yan bindigar suka tare hanyar, suka kuma yi awon gaba da su cikin daji. Wasu daga cikin waɗanda aka sace ’yan kasuwa ne da suka fito daga kasuwar mako ta New Bussa. Abin da ya faru a zaman...
A lokacin, sun yi wa motar ‘yansanda ruwan harsasai yayin da ɗaya daga cikin jami’an ya ji rauni, amma an garzaya da shi asibiti. Ya ƙara da cewa daga baya ‘yan bindigar sun sake tare wata hanya a gaba, inda suka sace fasinjoji a motoci uku. Abiodun, ya ce an tura ƙarin jami’an ‘yansanda tare da sauran jami’an tsaro da mafarauta don bin sahun ‘yan bindigar, da nufin ceto waɗanda aka sace da kuma cafke masu laifin. A wani samame daban, Abiodun ya bayyana cewa rundunar ‘yansandan tare da mafarauta sun kai farmaki wani dajin da ake zargin maɓoyar masu garkuwa, a cikin dajin Kokolo da ke Ƙaramar Hukumar Magama. A lokacin arangamar da aka yi da ‘yan bindigar, an...
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta ce kawo yanzu bata samu ba ta samu rubutaccen shirin zaman lafiya na shugaban Amurka Donald Trump kan Gaza ba. Mahmoud Mardawi wani babban jami’in kungiyar ta Hamas ya bayyana cewa har yanzu kungiyar ba ta samu daftarin shirin, wanda kafofin yada labaran Amurka suka wallafa bayanansa. Amma ya bayyana cewa tabas shirin wanda bai da garanti yana kusa da hangen nesa na Isra’ila. Dangane da furucin da Trump ya yi na kwance damarar kungiyar, ya fayyace cewa Hamas ba a taba amfani da makamanta ba da nufin kai hari ba, sai dai kawai domin kare ‘yancin cin gashin kan Falasdinu. Mardawi ya soki shirin na Trump, yana mai imani cewa wani yunkuri ne...
Shugaban kasar Madagaska Andry Rajoelina ya sanar da korar daukacin mambobin gwamnatinsa biyo bayan mummunar zanga-zangar da aka shafe kwanaki ana yi a kasar. A wani jawabi da ya yi na tsawon mintuna 17, ranar Litini, , Andry Rajoelina ya sanar da cewa ya ji kiran matasa tare da korar firaministansa da gwamnatinsa. Ya fara jawabinsane da jajanta wa wadanda suka rasa yan uwa da fatan samun sauki cikin gaggawa ga wadanda suka jikkata. Da yake jawabi ga matasan da suka fusata, ya bayyana cewa: “Na saurari muryoyinku, da bukatunku, Kuma ina ba da hakuri idan akwai mambobin gwamnati da ba su yi aikin da mutane suke tsammani […].” Shugaban ya bayyana a gidan talabijin na kasar cewa, “A bisa...
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci jihohin Arewa 19 da su tsaya ƙyam su jajirce su yi magana da murya ɗaya kan harkokin tsaro da tattalin arziki. Gwamnan ya jagoranci taron ranar farko ta bangaren Zuba Jari da Bunƙasa Masana’antu ta Arewacin Nijeriya a ranar Litinin a otel ɗin Abuja Continental. Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa Ƙungiyar Dattawan Arewa ƙarƙashin jagorancin Farfesa Ango Abdullahi ce ta shirya taron zuba jarin. Sanarwar ta ƙara da cewa, taken taron shi ne “Buɗe Dabarun Damarmaki”, kuma ya tattaro duk masu ruwa da tsaki a sassan Arewacin Nijeriya. A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya yaba wa Ƙungiyar Dattawan Arewa bisa jajircewar da...
Mutanen gari sun kama mutum uku da ake zargin suna da hannu a harin da ’yan bindiga suka kai ƙauyen Ƙadisau da ke Ƙaramar Hukumar Faskari da ke Jihar Katsina. Al’ummar yankin ne suka kama mutanen suka damƙa su ga jami’an tsaron al’umma na jihar domin gudanar da bincike. Yankin Ƙadisau da kewaye ya sha fama da hare-haren ’yan bindiga waɗanda suka kashe mutane da dama suka jikkata wasu tare da sace dabbobi masu yawa. Na baya-bayan nan shi ne wanda mahara suka kashe mutane uku suka yi garkuwa da mata biyar sannan suka yi awon gaba da dabbobi da ba san adadinsu ba. Abin da ya faru a zaman sulhun PENGASSAN da Matatar Ɗangote Netanyahu ya ba da haƙuri...
Gwamnatin Tarayya ta sanar da gobe Laraba a matsayin ranar hutu a ƙasar somin bikin cikar ƙasar shekara 65 da samun ƴancin kai. Cikin wata sanarwa da ministan cikin gida na ƙasar, Olibunmi Tunji-Oja ya fitar, ya taya ƴan Najeriya murnar cimma wannan ”babban matsayi”. Ministan ya kuma buƙaci ƴanƙasar su ci gaba da nuna kishin ƙasa da hadin kai da juriya, waɗanda ya ce su ne ke taimaka wa ƙasar wajen dunƙulewa tun lokacin samun ƴancin kai a 1960. A ranar 1 ga watan Otoban 1960 ne dai Najeriya ta samun ƴancin kai daga Turawan mulkin Birtaniya da suka yi mata mulkin mallaka.
Shugaban hukumar kula da fice ta kasa iran frud askari ya bayyana cewa yawan adadin huldar kasuwancin na kasashen waje na kasar iran yana ci gaba da gudana tsakaninta da fiye da kasashen duniya 100. Kuma yawansa ya kai dala biliyan 54.311a cikin wata shidan farko na wannan shakarar. Da yake hira da manema labarai ya fadi cewa a cikin wannan lokacin an samu kudi da yawansu yakai dala biliyan 25 da miliyan 944 a kayayyakin da ba na man fetur ba. Yace yawan kayayyakin da aka fitar a tsawon wannan lokaci ya kai tan miliyan da dubu 997, yayin da nauyin kayayyakin da aka shigo da su kuma ya kai tan miliyan dubu 18 zuwa 757. Da yake kwatantan...
A ranar Talatar nan ake sa ran ci gaba da tattaunawa tsakanin Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur (PENGASSAN) da Kamfanin Matatar Man na Ɗangote kan taƙaddamar da ke tsakaninsu. Ana sa ran za a ci gaba da zaman sulhun, wanda Gwamnatin Tarayya ta kira domin sasanta ɓangarorin ne zuwa da yamma. Hakan ta faru ne bayan an tashi taron a cikin tsakar daren ranar Litinin ba tare da an cimma wata matsaya ba. Gwamnatin Tarayya ta kira zaman sulhun ne bayan ƙungiyar PENGASSAN ta zargi Kamfanin Ɗangote da kora da kuma sauyin aikin mambobinta kimanin mutum 800. PENGASSAN ta yi barazanar yajin aiki muddin ba a dawo da ma’aikatan ba, a yayin da kamfanin ke cewa ga sallame su ne...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A ’yan watanni da suka gabata, matasa da yawa a Najeriya sun dukufa don ganin hakar su ta cimma ruwa wajen samun kudaden kirifto. Amma alamu na cewa a baya-bayan nan wasu daga cikinsu sun sare sun kuma saduda sun dawo daga rakiyar harkar. NAJERIYA A YAU: Abin Da Ɗangote, PENGASSAN Ba Su Yi Ba Don Magance Rikicinsu DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya yi nazari ne a kan dalilan wasu matasan na yin watsi da harkar kirifto. Domin sauke cikakken shirin, latsa nan
Buƙatun da ASUU ke nema sun haɗa da: sake duba yarjejeniyar 2009 tsakaninsu da gwamnati, samar da ƙarin kuɗaɗen bunƙasa jami’o’i, biyan bashin albashin da suke bi, da samar da ingantaccen tsarin kuɗi mai ɗorewa ga jami’o’i. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Fira Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ba wa Gwamnatin ƙasar Qatar haƙuri kan harin da ƙasarsa ta kai a birnin Doha, wanda ya yi ajalin wani jami’in tsaron Qatar. Netanyahu ya bayar da haƙuri ne a yayin wata tattaunawa da shugaban Amurka, Donald Trump ya shirya tsakaninsu da Fira Ministan Qatar, Mohammed Al-Thani. A saƙon da Netanyahu ya wallafa a X, ya ce, “Mai girma Fira Minista, ina sanar da kai cewa Isara’ila ta yi nadamar abin da ya faru na rasuwar wani ɗan ƙasarka a harin da muka kai,” da makami mai linzamina ranar 9 ga watan Satumba a birnin Doha. Fadar White House ta Amurka da Ma’aikatar Harkokin Wajen ƙasar Qatar sun tabbatar da tattaunawar, wadda Shugaba Donald...
Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran, wanda ya ziyarci kasar Lebanon domin halartar bikin zagayowar shahadar Sayyid Hassan Nasrallah, ya gana da babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qassem. Babban labarin jaridar Pars Today na cewa, Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran ya gana da babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qasem a ranar Lahadin da ta gabata. A wajen taron, Larijani ya jaddada goyon bayan Iran ga kasar Labanon da tsayin daka, inda ya yi misali da umarnin Imam Khumaini da Ayatullah Khamenei Jagoran juyin juya halin Musulunci tare da goyon bayan gwamnati da al’ummar Iran. Ya jaddada cewa Iran a shirye take ta ba da tallafi ga Lebanon da juriya “a kowane...
Malaman Kwalejin Kimiyya da Ƙere-ker ta Nuhu Bamalli da ke Zariya a Jihar Kaduna sun tsunduma yajin aiki. Ƙungiyar Malaman Kwalejin Kimiyya da Ƙere-kere (ASUP) reshen makarantar ta fara yajin aikin ne daga yau Talata, 39 ga Satumba, 2025. Ƙungiyar ta fara yajin aikin ne bayan zaman da ta yi da wakilan gwamnatin jihar, inda Babban Sakataren Gwamnatin Jihar, ya buƙaci su ƙara haƙuri, yana mai alamta cewa Gwamna Uba Sani ya ba da izinin biyan buƙatunsu. Sanarwar da Kwamared Usman Shehu Suleiman ya sanya wa hannu ta ce, “Daga Talata , 30 ga Satumba 2025 mu fara yajin aiki har sai abin da hali ya yi.” An shiga taron gaggawa kan takun saƙar PENGASSAN da Matatar Dangote ASUU ta...
An sanar da wannan matakin ne a yau 29 ga watan Satumba, 2025 a karkashin dokokin FIFA, amma kuma har yanzu SAFA suna da kwanaki goma domin daukaka kara a gaban kwamitin daukaka kara na FIFA. Tawagar Afirka Ta Kudu wadda Hugo Broos ke jagoranta a halin yanzu suna kan gaba a rukuninsu na C na neman cancantar shiga gasar cin kofin duniya, bayan da suka samu maki 17 daga wasanni takwas, amma kuma yanzu makin ya rikito zuwa 14 sakamakon zabtare maki 3 da hukumar FIFA ta yi musu. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin...
Yau Litinin ofishin ‘yan jarida na kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai don bayyana nasarorin da Sin ta samu a fannin ban ruwa a lokacin “shirin raya kasa na 14 na shekaru biyar” . Minista mai kula da harkokin ban ruwa Li Guoying ya bayyana cewa, tun daga farkon shirin, Sin ta fara samun ci gaba mai yawa a fannin gina kayayyakin ban ruwa. A shekarar 2022, kudaden da aka kashe wajen gina ayyukan ruwa sun kai sama da RMB yuan tiriliyan 1 a karon farko, kuma sun ci gaba da kafa tarihi har tsawon shekaru 3. A shekarar 2024, kudaden sun kai tiriliyan 1.3529 kwatankwacin dalar Amurka biliyan 190. Kuma ana sa ran yawan kudaden da za...
Shugabannin ƙungiyar manyan ma’aikatan man fetur da iskar gas ta Najeriya (PENGASSAN) da wakilan Matatar Dangote na halartar wani taron gaggawa tare da wakilan Gwamnatin Tarayya. Shugaban ƙungiyar PENGASSAN, Festus Osifo, tare da Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (TUC), Nuhu Toro, ne ke jagorantar ɓangaren ƙungiyoyin ƙwadago, yayin da Ministan Ƙwadago da Ayyuka, Maigari Dingyadi da wasu jami’ai ke wakiltar Gwamnatin Tarayya. Ya zama tilas ɗalibai su gabatar da ‘Project’ kafin rajistar NYSC — Tinubu Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Laraba Aminiya ta ruwaito cewa tun a ranar Lahadin da ta gabata ce Gwamnatin Tarayya ta gayyaci shugabannin PENGASSAN da na ɓangaren Matatar Dangote zuwa wannan taro sakamakon rikicin da ke tsakanin ɓangarorin biyu. Sai dai, duk da...
Gwamnatin Nijeriya ta ayyana ranar Laraba, 1 ga watan Oktoba, 2025 a matsayin ranar hutu albarkacin cikar ƙasar shekaru 65 da samun ’yancin kai. Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya fitar a madadin Gwamnatin Tarayya. Ɗalibar jami’ar IBB ta faɗi ta rasu FERMA ta ƙaddamar da aikin gyara tsohuwar hanyar Kano Tunji-Ojo ya taya ’yan Najeriya da ke zaune a nan cikin gida da ƙetare murnar zagayowar wannan rana mai tarihi, kamar yadda babbar sakatariyar ma’aikatar harkokin cikin gida, Dakta Magdalene Ajani ta bayyana a ranar Litinin. Ministan ya roƙi ’yan Nijeriya da su ci gaba da rungumar kishin ƙasa, haɗin kai da kuma juriya, domin a cewarsa, su ne ababen...
Wata ɗalibar aji biyu a sashen nazarin ƙwayoyin halittu da sunadarai na Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBU), Lapai da ke Jihar Neja ta riga mu gidan gaskiya. Aminiya ta ruwaito cewa, Fatima Adamu Muhammad, ta rasu ne bayan ta yanke jiki ta faɗi a wani matsuguninta da ke wajen makarantar. ASUU ta bayar da wa’adin tsunduma yajin aiki a faɗin Nijeriya FERMA ta ƙaddamar da aikin gyara tsohuwar hanyar Kano Rahotanni sun ce ta fara ƙorafin cewa ba ta jin daɗin jikinta da alamu na rashin lafiya, inda daga daga bisani ta yanke jiki ta faɗi. Sai dai bayan an garzaya da ita asibitin gwamnati na Lapai, likitoci suka tabbatar da cewa rai ya yi mata halinsa. Fatima Adamu Muhammad,...
Idan dai ba a manta ba, gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatar ilimi ta tarayya ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin babban sakataren ma’aikatar, Abel Enitan, domin duba buƙatar ƙungiyar ASUU, a wani yunƙuri na tabbatar da ci gaban jami’o’in. Sai dai har yanzu kwamitin bai fitar da wata sanarwa ko sakamakonsa ga jama’a ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Da yammacin yau Litinin ne ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya gudanar da taron nazari karo na 22, kan yadda za a sa kaimi ga mayar da addinan Sin zuwa addinan dake da salo na kasar. Yayin da ya jagoranci taron, babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, ya jaddada cewa, “Ya kamata mu tattara, da kuma amfani da darussan tarihi, mu mayar da hankali kan hakikanin ayyukan addinai na kasa, da sa kaimi ga mayar da addinan Sin zuwa addinan dake da salo na kasar, da kuma jagorantar addinai don daidaita al’umma mai ra’ayin gurguzu”. Xi Jinping ya kara da cewa, ana bukatar sa kaimi ga dunkulewar addinan kasar Sin, tare da kyawawan al’adun gargajiya na kasar bisa...
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU) ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin makonni biyu domin tsunduma yajin aiki muddin ta ci gaba da sakaci kan wasu buƙatu da take nema a biya. A sanarwar gargaɗi da ASUUn ta fitar yau Litinin, ta ce daga jiya Lahadi, 28 ga watan Satumba, za ta bai wa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 domin ta karkata akala kan buƙatun da take nema, ko kuma ta tsunduma yajin aikin gargaɗi na makonni biyu, inda daga nan zai rikiɗe zuwa na sai baba ta gani. An sallami Kwamishinar Mata ta Jihar Bauchi daga aiki ’Yan sanda sun kama kwayoyin N165.4m da makamai a Kano Shugaban ASUU, Farfesa Chris Piwuna, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da...
’Yan sanda sun kama miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 165.4 a watan nan na Satumba a Jihar Kano. Daga ciki, jami’an rundunar sun kama kwayoyin da kudinsu ya kai Naira miliyan 82.7 a unguwar Rimin Auzinawa, suka mika ga Hukumar Yaki da Ta’ammali da Miyagun Kwayoyi (NDLEA) domin kammala bincike da gurfanarwa a gaban kuliya. Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa rundumar ta kuma kama kwayoyin Tramadol da kudinta ya kai Naira miliyan 60.3 da kwayar Pregabalin ta Naira miliyan 22.4 da kuma sinki 523 na tabar wiwi da injinan tura kudi na POS guda biyar daga hannun wadanda ake zargi a sassan jihar. Kwamishinan ya ci gaba da cewa rundunar ta kama...
Gwamnatin Tarayya wajabta wa ɗaliban da suka kammala karatu mika kundin bincikensu na ƙarshe a matsayin sharaɗi kafin a tura su aikin yi wa kasa hidima (NYSC). Dokar za ta fara aiki ne daga ranar 6 ga Oktoba, 2025, kamar yadda Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya sanar. Ya bayyana cewa dokar ta shafi duk ɗaliban ajin ƙarshe da suka cancanci zuwa NYSC ko da kuwa a ƙasashen waje suka kammala karatu. Wannan yana daga cikin sauye-sauyen da Gwamnatin Tarayya ta yi wanda ya alaƙanta aikin Yi wa Ƙasa Hidima (NYSC) da Tsarin Tattara Bayan Ilimi ma Kasa (NERD). Ranar Laraba jirgin ƙasan Abuja-Kaduna zai dawo aiki Shekara 1 bayan rushewa, har yanzu ba gyara titin Kano–Maiduguri ba Bisa...
Shekara guda matafiya da direbobi a ƙauyukan Malori-Guskuri da Sabon Gari da ke Ƙaramar Hukumar Katagum a Jihar Bauchi na ci gaba da fama da wahala bayan da ruwan sama ya karya babban titin Kano–Maiduguri. A ranar 7 ga Agusta, 2024 ne ruwa ya cinye babbar hanyar a Malori-Guskuri, ya kuma yanke babban ɓangare na hanya. Mako guda bayan nan kuma wani ɓangaren ya rushe a Sabon Gari. Shekara guda da wata ɗaya bayan faruwar lamarin, wanda ya mayar wuraren da suka rushe sun koma tarkon mutuwa da ke haddasa haɗurra da suka kashe mutane da raunata wasu da dama. Wakilinmu da ya kai ziyara ya samu wani kamfanin gine-gine ya dawo Malori da kayan aikinsa. Mazauna sun tabbatar da...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Gwamnatin Tarayya ta gayyaci Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (PENGASSAN) da Matatar Ɗangote don a sasanta a yau. Hakan ya biyo bayan umarnin da ’yan ƙwadagon suka bai wa mambobinsu ne na shiga yajin aiki bayan da Matatar Ɗangote ta salami ma’aikata fiye da 800. Sai dai wasu masana suna ganin tun farko bai kamata lamarin ya kai ga haka ba, da an bi wasu hanyoyi. NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Gubar Cikin Abinci DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Cin Kifi Yadda Ya Kamata Waɗannan hanyoyi shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai binciko. Domin sauke shirin, latsa nan
Al’ummar unguwar Kuntau da ke Ƙaramar Hukumar Gwale a Jihar Kano, sun shiga jimami bayan rasuwar wani matashin limami, Salim Usman, wanda ake zargin ya rasu a hannun ’yan sanda. An kama Salim mai shekara 24 a gidansa a ranar 22 ga watan Satumba, jim kaɗan bayan jagorantar sallar Magariba. 2027: APC za ta ƙwace Kano ba tare da taimakon Kwankwaso ba – Jigon APC Sojoji sun kama mai yi wa Boko Haram safarar man fetur a Borno An zarge shi da siyan buhun fulawa, wadda aka ce an sace a bara. Mahaifinsa, Sheikh Adam Usman, ya bayyana cewa bidiyon na’urar CCTV ya nuna yadda jami’an ’yan sanda biyu suka yi wa ɗansa dukan tsiya a lokacin da suka zo...
Sabuwar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC daga jihar Kano ta samu nasararta ta farko a gasar Firimiyar ta Nijeriya (NPFL) bayan doke Kun Khalifa daga jihar Imo a wasan mako na 5 da aka buga a birnin Aba. Wannan shi ne karon farko da ƙungiyar ta samu nasara tun bayan haurowarta gasar. A minti na 14 da fara wasan ne Kun Khalifa suka fara zura ƙwallo a ragar Barau FC. Sai dai minti biyu kacal bayan haka, Yahaya Ibrahim ya farke wa Barau FC kwallo, wanda ya buɗe musu ƙofar dawowa cikin wasan. Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa Barau Jibril Ya Yi Alhinin Rasuwar...

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Jaddada Aniyarta Ta Rashin Amincewa Da Duk Wani Takunkumi Kan Iran
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta jaddada cewa: Ba za a yarda da ƙoƙarin maido da kudurori da suka ƙare ba kan Iran Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta tabbatar da cewa: Yunkurin da kungiyar Tarayyar Turai Troika da Amurka ke yi na maido da kudurorin Majalisar Dinkin Duniya da suka kare kan Iran, ba abu ne da za a amince da su ba. Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta fitar da sanarwar mayar da martani ga ikirarin da kasashen Turai uku da Amurka suka yi na maido da kudurorin kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da suka kare kan Iran. Ma’aikatar ta yi la’akari da yin amfani da hanyar warware takaddama da aka tanada a cikin yarjejeniyar hadin gwiwa game da...
A yau Lahadi ne aka gudanar da biki mai taken “Bude sabon babi a sabon zamani: Bikin zurfafa hadin gwiwa tsakanin CMG da bangarori daban daban na Macao” a yankin Macao na kasar Sin. Shugaban babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG Shen Haixiong, ya halarci bikin tare da gabatar da jawabi. Cikin jawabin nasa, Shen Haixiong ya ce “A yau CMG ya sake kaddamar da ayyukan hadin gwiwa da dama tare da bangarori daban daban na Macao, kamar gabatar da wani fim mai bayana labarai mai suna “Macao: Gidan adana kayayyakin tarihi a fili”, da kuma fitar da “Gadon ruhin kishin kasa: Hanyar yawon shakatawa ta wuraren tarihi dake nuna kishin kasa na Macao”, ta yadda...
Dakarun Operation Haɗin Kai su kama wani mutum da ake zargi yana kai wa Boko Haram man fetur a Jihar Borno. Wanda aka kama, mai suna Thomas James, mai shekaru 54, an cafke shi ne ranar 23 ga watan Satumba a kusa da sansanin Forward Operating Base da ke Ngwom. PENGASSAN ta tsunduma yajin aiki kan korar ma’aikata a kamfanin Dangote Jami’ar Bayero ta sallami ɗalibai 57 kan maguɗin jarrabawa An same shi da kwalabe 23 na man fetur da ya ɓoye cikin jaka a lokacin da yake tafiya daga Maiduguri zuwa Gamboru Ngala. Bincike ya gano cewa yana yi wa Boko Haram safarar man fetur, sai dai wannan karon an yi nasarar kama shi. Wanda dai ba shi ne...
Yayin da yake bayani kan muhimmancin wannan shiri, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ya ce: “Wannan Cibiyar wata gagarumar alama ce ta kudurin Gwamnatin Jihar Kaduna na bunkasa koyon sana’o’i, karfafa matasa, da haɓaka tattalin arziki. Yace An zaɓi fannonin sana’o’i 14 ne cikin hikima domin su magance manyan bukatun ƙwararrun ma’aikata a bangarorin gine-gine, makamashi, fasahar zamani (ICT), kula da baƙi, da harkokin ƙirƙira. Muna da yakinin cewa waɗanda suka kammala karatu a wannan Cibiyar ba kawai za su samu ayyukan yi ba ne, har ma za su zama masu dogaro da kai kuma su samar da dama ga wasu.” Shima Shugaban Cibiyar, Malam Husaini Haruna Muhammad, ya jaddada muhimmancin da horon ke...
Wasu mutane da ake kyautata zaton ‘yan fashin teku ne sun yi awon gaba mutum 17 a wani kwale-kwale da ke kan iyakar teku a jihohin Akwa Ibom da Kuros Riba. Lamarin ya faru ne a lokacin da fasinjojin suka taso daga wani ƙauye a kan iyakar jihohin biyu, inda ‘yan fashin suka afka wa kwale-kwalen a cikin nasu jirgin ruwa, sannan suka yi awon gaba da fasinjoji 17. Matatar Dangote ta ci gaba da sayar da man fetur a naira Nukiliya: MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman karayar tattalin arziki Kwale-kwalen na wani kamfani ne da ke aikin jigilar fasinjoji tsakanin jihohin biyu a kan teku. A ‘yan shekarun baya matsalar satar mutane da garkuwa da su ta...
Wasu mutane da ake kyautata zaton ‘yan fashin teku ne sun yi awon gaba mutum 17 a wani kwale-kwale da ke kan iyakar teku a jihohin Akwa Ibom da Kuros Riba. Lamarin ya faru ne a lokacin da fasinjojin suka taso daga wani ƙauye a kan iyakar jihohin biyu, inda ‘yan fashin suka afka wa kwale-kwalen a cikin nasu jirgin ruwa, sannan suka yi awon gaba da fasinjoji 17. Matatar Dangote ta ci gaba da sayar da man fetur a naira Nukiliya: MDD ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkuman karayar tattalin arziki Kwale-kwalen na wani kamfani ne da ke aikin jigilar fasinjoji tsakanin jihohin biyu a kan teku. A ‘yan shekarun baya matsalar satar mutane da garkuwa da su ta...
Tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya yi zargin cewa, cikin watanni shida, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya samu karin kaso daga gwamnatin tarayya fiye da yadda ya samu a cikin shekaru 8 da ya yi yana gwamna. Batun rabon kuɗaɗen wata-wata ga Jihohin dai ya zama abun muhawara a karkashin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu. Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa? Gwamna Yusuf Ya Aike Da Sunayen Kwamishinoni Zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano “A yau zan iya bugun ƙirjina kuma kowanne daga cikin gwamnonin nan zai iya tabbatar da cewa, rabon da ake bai wa jihohin ya ninka sau uku, kuma akwai l isassun kuɗaɗe daga ƙananan hukumomi.” in ji Ganduje Da yake...
Majalisar Dinkin Duniya ta sake ƙaƙaba wa Iran takunkumai na karayar tattalin arziki bayan gaza cimma matsaya a tattaunawar ƙarshe kan shirin nukiliyarta da manyan ƙasashen yammacin Turai. Birtaniya, Faransa da Jamus ne suka bijiro da batun maido da waɗannan takunkuman a taron kwamitin Sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya, wanda aka yi kan saɓa yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015 da Iran ta yi. NECO ta sake jaddada nasarar ɗaliban Kano a jarrabawar bana Matatar Dangote ta ci gaba da sayar da man fetur a naira Haka kuma, ƙasashen uku sun gargaɗi Tehran kan ɗaukar matakan da za su ƙara dagula lamarin. “Sake ƙaƙaba takunkuman Majalisar Dinkin Duniya ba yana nufin ƙarshen diflomasiyya ba ne,” in ji ministocin harkokin wajen ƙasashen uku...
Firaministan Nijar Mahaman Lamine Zein ya yi Allah wadai da yadda kasashen ketare ke da hannu wajen tada zaune tsaye a yankin Sahel. Lamine Zein, ya bayyana hakan a jawabin da ya gabatar da a zauren babban taron MDD karo na 80 dake gudana a birnin New York. Nijar ta kuma yi Allah wadai da kisan kiyashin Isra’ila a Gaza, da kuma hare haren Isra’ilar kan Iran da Qatar, da kuma yadda ake nuna halin ko in kula game da rikicin Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo da Sudan dama yankin Sahel tare da hadin bakin wasu manyan kasashen yamma a nahiyar Afrika. Fira ministan na Nijar, Ya kuma kara da cewa gwamnatin Nijar da takwarorinta na Burkina da Mali, a sun sha...
Maude dan shekara 40, kwararren lauya ne, kuma haziki wanda ya kammala karatun digiri a fannin shari’a daga babbar jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria. Shi mamba ne a kungiyar lauyoyin Nijeriya da kuma a Cibiyar Masu sasantawa ta Nijeriya. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ƙasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa jiragenta da ke jigilar fasinjoji daga Abuja zuwa Kaduna, za su koma aiki a mako mai zuwa. Mai magana da yawun NRC, Callistus Unyimadu, ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da hukumar ta fitar a jiya Asabar, duk da yake bai sanar da haƙiƙanin ranar da za a koma aikin ba. Tun daga shekarar 1899 Faransa take haddasa mana rikici — Nijar Ɗalibi ya kashe malaminsa har lahira a Kuros Riba Callistus, ya ƙara da cewa matakin ya biyo bayan nasarar kammala gyare-gyare da bincike a ɓangaren da aka samu matsala a baya-bayan nan. A cewarsa, hukumar na yin aiki ba tare da gajiyawa ba don...
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta sake jadda yin Allah-wadai da kisan tsohon shugaban kungiyar Hizbullah Sayyed Hassan Nasrallah, inda ta bayyana cewa, matakin ya kasance karara a matsayin keta dokokin kasa da kasa da kuma tsarin Majalisar Dinkin Duniya. An fitar da sanarwar ne a wannan Asabar, a daidai lokacin da ake bukin cika shekara guda da kisan gillar da aka yi wa Shahid Nasrallah da Sayyed Hashem Safieddine, wadanda aka kashe a shekarar da ta gabata a wasu hare-hare da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a Beirut. A cikin sanarwar da ta fitar, ma’aikatar harkokin wajen kasar ta kira kisan gillar a matsayin wani babban ta’addanci da nufin yi wa kasa mai cin gashin kanta mamba a...
Gwamnatin Jamhuriyyar Nijar ta zargi Faransa da ɗaukar shekaru tana haifar da rikice-rikice da rashin tsaro a ƙasar da maƙotanta na yankin Sahel, tun daga shekarar 1899. Firaministan Nijar, Ali Lamine Zeine, ne ya yi wannan furuci ranar Asabar yayin gabatar da jawabi a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80 (UNGA 80) da ke gudana a birnin New York na ƙasar Amurka. Ɗalibi ya kashe malaminsa har lahira a Kuros Riba Ma’aikatan jinya sun tsunduma yajin aiki a Zamfara Lamine Zeine ya zargi Faransa da yin amfani da ƙungiyoyin “ta’addanci” domin tayar da rikici da haddasa rashin tsaro a ƙasarsa da maƙotanta na yankin Sahel, inda ya buƙaci mahukunta a Paris su “tuna tare da ɗukar alhakin laifukan...
Gwamnatin Jamhuriyyar Nijar ta yi zargin cewa tun daga shekarar 1899 Faransa take fafutikar tayar da rikici da haddasa rashin tsaro a ƙasar da maƙotanta na yankin Sahel. Firimanistan Jamhuriyyar Nijar, Ali Lamine Zeine, ya yi wannan caccakar ce kan Faransa a ranar Asabar yayin da yake gabatar da jawabi a Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA 80) da ke gudana a birnin New York na Amuka. Ɗalibi ya kashe malaminsa har lahira a Kuros Riba Ma’aikatan jinya sun tsunduma yajin aiki a Zamfara Lamine Zeine ya zargi Faransa da yin amfani da ƙungiyoyin “ta’addanci” domin tayar da rikici da haddasa rashin tsaro a ƙasarsa da maƙotanta na yankin Sahel, inda ya buƙaci mahukunta a Paris su “tuna tare da...
Sau da yawa wasu mutane suna raina wanka da gyara jikinsu, Inda suka fi gane wanke jiki ko rashin amfani da turare, bayan kuma tsafta tana daga cikin imani. Abubuwan da ke kawo wari mai tashi ya addabi wadanda ke kusa; sun hada da rashin wanke jiki da lungu da sako a yayin wanka. Sannan rashin saka turare a jiki yana haifar da wari ko da ana wanka. Bugu da kari wasu suna yin kwana hudu, biyar, har zuwa sati daya ba tare da sun yi wanka ba. Kayan jiki ma wasu suna maimaita saka su fiye da sau biyu ko uku a cikin sati daya. Hanyoyin da za a bi domin magance matsalar wari mai tashi su ne; yawan...
Wani ɗalibi mai suna Ogbeche, ya kashe malaminsa Oshen, a makarantar sakandire da ke garin Ugboro, da ke Ƙaramar Hukumar Bekwarra a Jihar Kuros Riba. Rahotanni sun nuna cewa malamin ya yi ƙoƙarin raba faɗa tsakanin Ogbeche da wani ɗalibi. Ma’aikatan jinya sun tsunduma yajin aiki a Zamfara Matatar Ɗangote ta dakatar da sayar da fetur a farashin Naira Sai dai a fusace, ɗalibin ya fisge taɓarya daga hannun wata mata, ya buga wa malamin a kai, wanda hakan ya sa ya faɗi sumamme. Duk da garzayawa da shi da aka yi zuwa asibiti, likitoci sun tabbatar da mutuwarsa. Wata ganau mai suna Lizzy ta ce: “Malamin kawai yaje rabon faɗa ne, amma Ogbeche ya fusata ya ɗauki taɓarya ya...
Yawan ribar da manyan kamfanoni na kasar Sin suke samu ta karu da kashi 0.9 cikin 100 a mizanin shekara-shekara a cikin watanni takwas na farkon shekarar 2025, lamarin da ya farfado da raguwar da aka samu da kashi 1.7 cikin 100 a tsakanin watannin Janairu zuwa Yuli, kamar yadda alkaluman hukuma suka nuna a yau Asabar. Jimillar ribar da kamfanonin da ke samun makudan kudin shiga na kasuwanci a shekara na akalla yuan miliyan 20 (kimanin dalar Amurka miliyan 2.81) ta kai kusan yuan tiriliyan 4.7 a cikin watannin takwas, a cewar hukumar kididdiga ta kasar Sin. A cikin watan Agusta, ribar da manyan kamfanonin suka samu ta farfado sosai, inda ta karu da kashi 20.4 cikin 100 a...
Ƙungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta Najeriya, reshen Jihar Zamfara, ta ce sun shiga yajin aiki na kwanaki shida a matsayin gargaɗi. Shugaban ƙungiyar, Sani Shehu, ya ce sun ɗauki wannan mataki ne domin tunatar da gwamnati batun sabon tsarin albashi na ma’aikatan lafiya. AGILE ta raba kayan karatu da sana’o’i a cibiyoyi 54 a Gombe HOTUNA: An kai gawar Arase Benin domin yi mata jana’iza Ya ce duk da cewa gwamnati ta amince da tsarin CONHESS na ma’aikatan lafiya, amma har yanzu ta kasa aiwatar da tsarin CONMESS na likitoci. A baya, ƙungiyar ta fara yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai a ranar 11 ga watan Satumba, amma ta dakatar bayan kwana ɗaya saboda alƙawarin da gwamnati ta yi...
Ƙungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta Najeriya, reshen Jihar Zamfara, ta ce sun shiga yajin aiki na kwanaki shida a matsayin gargaɗi. Shugaban ƙungiyar, Sani Shehu, ya ce sun ɗauki wannan mataki ne domin tunatar da gwamnati batun sabon tsarin albashi na ma’aikatan lafiya. AGILE ta raba kayan karatu da sana’o’i a cibiyoyi 54 a Gombe HOTUNA: An kai gawar Arase Benin domin yi mata jana’iza Ya ce duk da cewa gwamnati ta amince da tsarin CONHESS na ma’aikatan lafiya, amma har yanzu ta kasa aiwatar da tsarin CONMESS na likitoci. A baya, ƙungiyar ta fara yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai a ranar 11 ga watan Satumba, amma ta dakatar bayan kwana ɗaya saboda alƙawarin da gwamnati ta yi...

Tawagar Gwamnatin Tsakiya Na Ci Gaba Da Ziyartar Jami’ai Da Mazauna Yankuna Da Dama Na Jihar Xinjiang
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Tabbas, ko a zamanin yau ma, aikin raya tattalin arziki ba ya rabuwa da wahalhalu. Misali, a cikin gidajen da ake kiwon jatan lande, dole ne mutane su jure yanayi mai zafi da ya kan kai sama da digiri 40 na ma’aunin Celcius, da kuma tarin sauro dake cizon mutum. Har ila yau, akwai wasu kifayen da ake kiwonsu, misali Mullet, wadanda mazauna yankin Xinjiang ba su saba da cinsu ba, don haka ana bukatar karin kokari a fannin tallarsu a kasuwa.Duk da haka, lokacin da ake magana kan makomar harkokinsu, masu samar da kayan noma na Alar suna cike da kwarin gwiwa. Wani mai kiwon kifi ya bayyana cewa, “Bisa fasahar noman abincin ruwa da muka bunkasa a...
Yayin da aka ce jam’iyyun siyasa a jamhuriya ta farko, sun fi karkata kan yanki, an yi yunkurin kafa jam’iyyun kasa a jamhuriya ta biyu da gangan. A wancan jamhuriyar (1979–1983), manyan jam’iyyun siyasar Nijeriya su ne GNPP, NPN, NAP,NPP, PRP, da kuma UPN. Duk da cewa, jam’iyyun sun banbanta a akida; amma ana ganin jam’iyyun UPN da PRP, a matsayin na masu fafutuka da kuma jajircewa, domin kuwa jam’iyyar UPN ta tsaya tsayin-daka wajen aiwatar da manufofinta. An gina tsarin jam’iyyar bisa manyan manufofi hudu kamar haka: ilimi kyauta tun daga makarantar reno har zuwa manyan makarantu, harkar kiwon lafiya kyauta, hadin gwiwar karkara da ci gabanta da kuma samar da cikakkun ayyukan yi masu dorewa. Wadannan alkawura, an...
A jawabinsa na maraba da mahalarta taron, Shugaba kuma Wakilin ofishin hukuma da ke Abuja wanda har ila yau wakilin UNESCO, na Nijeriya, Mista Mendy Albert, wanda Misa Manish Joshi ya wakilta, ya ce tsarin da akwai kwas na mako 10- ta kafar sadarwa ta zamani wanda aka kammala a watan Yuli, an shirya shi ne domin a karawa masu halartar taron yadda za su bunkasa da zamantar da ilimin koyon sana’a da fasaha. Yace TBET wata babbar madafa ce da zata iya taimakawa matasa wajen koya masu dabarun da suka dace, wadanda ta haka ne za su damar tsayawa da kafafunsu dpomin samun bunkasar zamantakewa da tattalin arziki. A nata jawabin,darekta ta fasaha da kimiyya ma’aikatar ilimi ta tarayya,...
A wani labarin kuma, Jami’an NDLEA sun kama wata ‘yar kasuwa mai shekaru 38, Okolonkwo Ebere Theresa, a ranar Lahadi, 14 ga watan Satumba, bayan da jami’an tsaron jiragen sama na hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta Nijeriya tare da hadin gwiwar jami’an hukumar NDLEA suka gano 1.40kg na methamphetamine da ta boye a cikin rigarta domin shiga jirgin saman Katar. A tashar NAHCO da ke filin jirgin saman Legas a ranar Litinin, 15 ga Satumba, NDLEA ta kama wani kayyakin abinci mai kunshe da dauri 40 na methamphetamine mai nauyin kilogiram 2.30 wanda ya nufi Hong Kong ta hanyar jirgin saman Turkish Airlines. An kama wani da ake zargi mai shekaru 59, Umelo Ifeanyi Benatus,...
Gabanin shekarar 2005 da gwamnatin Kano ta hana sana’ar haya da babur saboda matsalar tsaro da ta kunno kai jihar, jigilar fasinjoji ta ta’allaƙa ne da motocin haya na hayis, ko tasi, a kuma farashi mai sauƙi. Sai dai sannu a hankali, waɗannan motocin hayar suna neman zama tarihi musamman a birane saboda zuwan babura masu ƙafa uku, waɗanda aka fi sani da ‘A Daidaita Sahu’ a lunguna da saƙo. Wata ƙididdiga da Hukumar Samar da Kuɗaɗen Shiga ta Jihar Kano ta fitar, na nuna gwamnatin jihar tana samun aƙalla Naira miliyan shida a kullum daga harajin Naira 100 da ta sanya wa masu sana’ar A Daidata Sahu — wanda a shekara ya kai Naira biliyan 2.1. Haka kuma...
Ya kara da cewa wadanda ake zargin suna nan a gidan yari kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da su a gaban kotu domin hukunci. Kwamishinan ’Yansandan Jihar, CP Bello M. Sani, ya yaba wa kwazon da DPO da ’yan banga suka yi da gaggawa, inda ya jaddada muhimmancin hadin kan ‘yansanda da al’umma wajen magance miyagun laifuka. Ya kuma tabbatar wa mazauna Jihar Kebbi cewa, rundunar ‘yansandan ta jajirce wajen kawar da masu aikata laifuka da samar da yanayi mai tsaro. Daga nan sai ya bukaci jama’a da su sanya ido tare da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin daukar matakin gaggawa. Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi ta kama wasu...
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya sauka a Lagos a jiya Juma’a domin ziyarar aiki yayin da ƙasar ke shirin bikin cikar shekaru 65 da samun ƴancin kai daga turawan mulkin mallaka. A cewar kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, Tinubu ya tafi Legas ne bayan ya halarci naɗin sabon Olubadan na Ibadanland, Oba Rashidi Ladoja, a garin Ibadan, jihar Oyo. Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman Yayin da yake a Lagos, shugaban ƙasa zai gana da manyan ƴan kasuwa da jiga-jigai a ɓangaren gwamnati domin tattaunawa kan ci gaban tattalin arzikin ƙasa. Haka kuma, a ranar Talata, 30 ga Satumba, zai ziyarci...
Wakilan ƙasaahen duniya sun ƙaurace wa jawabin Shugaban Ƙasar Isra’ila Benjamin Netanyahu, a taron Majalisar Ɗinkin Duniya domin su nuna goyon bayansu ga al’ummar Palasɗinawa. Fiye da rabin wakilan da suka halarci Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) sun miƙe tare da ficewa daga zauren taron ne a yayin da Mista Netanyahu yake shirin gabatar da jawabin ƙasarsa ta Isra’ila. Zauren taron ya kasance kusan wayan, in banda ’yan jarida da jami’an MƊD da wasu tsirarun wakilan ƙasashe da suka rage a ciki a lokacin jawabin Mista Netanyahu wanda Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC) ta ba da umarnin kamo shi domin gurfanarwa kan laifukan yaƙi a Zirin Gaza inda dakarun Isra’ila suka kashe mutane kimanin 79,000, akasarinsu ƙananan...
Ya kara da cewa, duba da irin dimbin Kogunan da ake da su a wannan kasa, idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, za a iya bunkasa fannin na kamun kifi a Nijeriya. Omoragbon ya ci gaba da cewa, kalubalen da ake ci gaba da fuskanta a halin yanzu shi ne, na karancin kudade da kuma ci gaba da samun hauhawar farashin abincin da ake ciyar da kifin, wanda wannnan babban kalubale ne da masu sana’ar ke ci gaba da fuskanta a kasar. “Muna sane da cewa, babban kalubalen da masu sana’ar a kasar nan ke ci gaba da fuskanta shi ne, karancin kudade tare da kuma ci gaba da samun hauhawar farashin abincin kifin, amma za mu...
Hukumar jin daɗin Alhazai ta ƙasa (NAHCON) ta sanar da farashin aikin Hajjin 2026, inda aka samu ragin kaso 9.7% cikin ɗari idan aka kwatanta da farashin Hajjin bara 2025. A cewar sanarwar da shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Sale Usman, ya fitar ranar Juma’a da daddare, alhazai daga gundumar Maiduguri–Yola (Borno, Yobe, Adamawa da Taraba) za su biya N8,118,333.67, yayin da sauran jihohin Arewa za su biya N8,244,813.67. A gefe guda kuma, alhazai daga jihohin Kudu za su biya N8,561,013.67. Wannan na nufin cewa kowanne mai niyyar tafiya Hajji a bana zai samu ragin kimanin N200,000 ƙasa da farashin 2025. EFCC Ta Kama Daraktocin NAHCON 2 Kan Zargin Karkatar Da Kuɗin Hajjin 2025 Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77...
Har ila yau, ya kara da cewa; kudaden shigar da za a samu, za su karu zuwa dala 657, inda kuma za a kara samun sama da tan miliyan 1.2. Ya ci gaba da cewa, albarkatun da Nijeriya ta ke da su, kashi 20 a cikin dari ne kacal na miliyoyin hektar noman da ake da su a wannan kasa ake nomawa, wanda kuma na hektar noman rani ta haura miliyan uku. Ministan ya kuma sanar da cewa, bisa sauye-sauyen da ake ci gaba da samar wa bangaren shiyoyin sarrafa amfanin gona don samun riba, samar da kayan aiki da kudden aikin noma da bankin manoma ke yi da sauransu. Kyari ya kuma bai wa masu son zuba hannun jarin...
Bisa sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, ” shugaban kasa ne zai nada shugaban INEC da mambobin hukumar zabe ta kasa, sannan majalisar dattawa ta tabbatar da su.” Dangane da tanadin da ke cikin tsarin mulki, Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya tanadi jerin sunayen ‘yan takara da za su meye gurbin Yakubu. Da yake jawabi kan tsammanin jam’iyyar APC mai mulki, daraktan yada labarai, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa yayin da jam’iyyar ke nufin lashe duk zabe, tana jaddada bukatar samun yin aldaci ga kowa. Ibrahim, a cikin wata hira, ya bayyana cewa, “A matsayinmu na jam’iyya, abin da muka sa a gaba shi ne samun nasarar cin...
Yayin da ƙasashe irin su Birtaniya, Kanada da Ostareliya suka amince da kafa ƙasar Falasṭinu, ana tsammanin samun ƙarin wasu ƙasashe. Shugaban Falasɗinu, Mahmud Abbas, ya yaba da wannan mataki tare da kira ga sauran ƙasashe su nuna irin wannan goyon baya. Zargin ɓatanci: Kwamitin Shura na Kano ya fara sauraron koke-koke kan Malam Triumph An gano yarinya da aka sayar ₦3.7m a Ondo Yawancin ƙasashen Afirka sun riga sun amince da Falasdɗinu tun shekarun 1980. Shugabanni irin su Thomas Sankara da Nelson Mandela sun taɓa danganta gwagwarmayar Falasɗinawa da irin ta Afirka na neman ’yanci. Amma har yanzu akwai ƙasashe biyu da ba su amince da kafa ƙasar Falasɗinu ba; wato Kamaru da Eritrea. Kamaru Kamaru tana da alaƙa...
Da Baba Zube ya mike don yi jawabi bayan an gabatar da shi, sai ya yi waiwaye Wanda masu iya magana suka ce, adon tafiya. Ya kawo takaitaccen bayani kan gwamnati a kasar da yau ake kira Nijeriya. Ya tabo, Daular Usmaniyya mai hedikwata a Sakkwato, wadda kuma ita ce daula ta karshe da Turawa suka rusa a kasar nan. Kuma ya bayan cewa Daular Borno da ta Kwararrafa ne kawai a Arewa ba su cikin Daular Usmaniyya. Sai Kudu maso Yamma da ya zauna a karkashin Daular Yarbawan Oyo. Kudu maso Kudu kuma Daular Benin, yayin da Yankin Kudu maso Gabas ke rayuwa karkashin kananan sarakunan kabilar Ibo. Ya yi takaitaccen bayani kan yadda Turawan Mulkin Mallaka suka ci...

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon
Rahotanni daga ofishin kula da zirga-zirgar kumbuna masu dauke da ’yan sama jannati a sararin samaniya na kasar Sin, sun ce da misalin karfe 1 da minti 35 na sanyin safiyar yau Jumma’a 26 ga wata, bisa hadin-gwiwar dan sama jannati Chen Dong dake cikin kumbo, sauran ’yan sama jannatin kumbon Shenzhou-20 guda biyu, wato Chen Zhongrui da Wang Jie, sun gudanar da ayyuka har na tsawon sa’o’i 6 a wajen kumbon, inda suka kammala ayyukansu bisa shiri. Ya zuwa yanzu, Chen da Wang sun riga sun koma sashin gwaje-gwaje na Wentian lami lafiya, al’amarin da ya shaida babbar nasarar da suka samu wajen gudanar da ayyuka a wajen kumbon. Yayin da suke wajen kumbon, ’yan sama jannatin biyu sun...
Gwamnatin Jihar Kano ta miƙa ƙorafe-ƙorafen da aka yi a kan Malam Shu’aibu Abubakar, wanda aka fi sani da Triumph, ga Kwamitin Shura na Jihar don ɗaukar matakin da ya dace. Sakataren Gwamnatin Jihar ne, ya tura ƙorafe-ƙorafen a ranar Juma’a, inda kwamitin ya fara zama domin sauraronsu. ’Yan Najeriya da tauraronsu ya haska a Ballon d’Or Yadda ’yan haya za su samu ragin N500,000 a shekara A cewar kwamitin, za a gayyaci masu ƙorafi da Malam Triump domin su gabatar da hujjoji. Masu ƙorafi za su fayyace abubuwan da suke tuhumar malamin, yayin da shi kuma za a ba shi damar kare kansa. Bayan haka kwamitin zai tattauna bisa ƙa’idojin shari’ar Musulunci. Sakataren kwamitin, Shehu Wada Sagagi, ya shaida...
A ranar Litinin aka gudanar da bikin bayar da kyautar Ballon d’Or a Birnin Paris, inda ake karrama fitattun ’yan ƙwallon duniya. A bana, Ousmane Dembele na Ƙasar Faransa da PSG ne, ya lashe kyautar maza, yayin da Aitana Bonmati ta Spaniya ta lashe ta mata karo na uku a jere. An gano yarinya da aka sayar ₦3.7m a Ondo Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan Abin farin ciki ga Najeriya shi ne, mai tsaron ragar Super Falcons, Chiamaka Nnadozie, ta zo ta huɗu a jerin mata, wanda shi ne matsayi mafi girma da wata ’yar Najeriya ta taɓa samu. Ga jerin ’yan Najeriya da suka taɓa shiga cikin jerin waɗanda suka fafata neman kyautar Ballon d’Or:...
Ita kuwa Abuja Babban Birnin Nijeriya ta samu wasu marasa lafiya guda biyu da wani nau’in zazzabi da ke sa mutane zubar da jini amma hukumomi sun ce ba a sami marasa lafiyar da Lassa ko kuma Ebola ba. Cuta mai zagwanye naman jikin dan’adam Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya, NAN ya rawaito cewa cutar da ta yi sanadiyyar mutuwar mutum bakwai a Jihar Adamawa tana faraway ne daga kuraje. Daga nan kuma sai su fashe tare da zagwanyewa inda wani lokacin ma suke side fatar har su tarar da kashi a gabar da cutar ta shafa. Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO ta bayyana cutar kuraje ta Buruli Ulcer da daya daga cikin cutukan da ba a fiya mayar da...
Jami’an ’yan sanda a Jihar Ondo sun kuɓutar da wata yarinya ’yar shekara huɗu da ta ɓace tare da gano wasu masu fataucin yara da ke gudanar da ayyukan su a yankunan Jihohin Ondo, Delta da Anambra. An fara shari’ar ne a ranar 3 ga Fabrairu, 2025, lokacin da Sunday Kingsley da ke yankin Alagbaka Extension a garin Akure, ya ruwaito cewa ’yarsa Jesinta, ta ɓace ne a lokacin da take tare da mahaifiyarta Sunday Happiness. Gwamnatin Kebbi ta sake jaddada goyon bayanta ga hukumomin tsaro Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar, Olusola Ayanlade ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar kuma aka sanarwa manema labarai a Akure ranar...
Sakataren Majalisar Koli ta Tsaron kasar Iran ya bayyana cewa, Tehran za ta katse yarjejeniyarta da take yi da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, tare da daina bada hadin kai ga binciken makamai na kasa da kasa, idan har aka aiwatar da tsarin “sake dawo mata da takunkuman Majalisar Dinkin Duniya. Sakataren Majalisar ta Iran Ali Larijani ya sake nanata kudurin Iran na cewa ba da ta niyyar yin amfani da makamin nukiliya – ko dai a yanzu ko a nan gaba. Ya kuma ce ayyukan wuce gona da iri da Amurka da Isra’ila suka yi kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku a watan Yuni ya sanya tattaunawar ta zama “bazara”. Yau Juma’a ne kwamitin sulhu na...
Gwamnatin Jihar Kebbi ta sake jaddada ƙudirinta na ci gaba da tallafawa dukkan hukumomin tsaro da ke yaƙar ’yan bindiga da ta’addanci a jihar. Kwamishinan yaɗa labarai da al’adu na Jihar, Alhaji Yakubu Ahmed Birnin Kebbi, ne ya tabbatar da hakan lokacin da ya tarbi Daraktan Yaɗa Labaran Sojoji, Birgediya Janar T. I. Gusau, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa da ke Birnin Kebbi. Naɗin Olubadan: Tinubu da manyan jami’ai sun ziyarci Ibadan Sojoji sun kashe ’yan ta’adda tare da ƙwato makamai a Neja Alhaji Yakubu ya bayyana irin muhimman tallafin da Gwamna Nasir Idris ke bayarwa tun daga lokacin da ya fara mulki shekaru biyu da suka gabata, wanda ya haɗa da kayayyakin aiki da alawus...
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
Dakarun rundunar sojoji ta 22 Armored Brigade da ke aiki a ƙarƙashin Operation Park Strike V tare da haɗin gwiwar Jami’an tsaron gandun daji sun kashe wasu ’yan ta’adda da ba a tantance adadinsu ba a dajin Kainji da ke Ƙaramar hukumar Borgu a Jihar Neja. Hakazalika an samu nasarar ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3 da babura 4 daga hannun maharan. Babu wata jam’iyya dana ke shirin komawa — Kwankwaso ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a Masallaci a Zamfara Muƙaddashin Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar soji ta 22 da ke Ilorin, Captain Stephen Nwankwo, a wata sanarwa ne ya tabbatar da faruwar lamarin ya kuma ce, ɗaya daga cikin jami’an da suke kula da gandun dajin yankin...
Dakarun rundunar sojoji ta 22 Armored Brigade da ke aiki a ƙarƙashin Operation Park Strike V tare da haɗin gwiwar Jami’an tsaron gandun daji sun kashe wasu ’yan ta’adda da ba a tantance adadinsu ba a dajin Kainji da ke Ƙaramar hukumar Borgu a Jihar Neja. Hakazalika an samu nasarar ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda 3 da babura 4 daga hannun maharan. Babu wata jam’iyya dana ke shirin komawa — Kwankwaso ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a Masallaci a Zamfara Muƙaddashin Daraktan hulɗa da jama’a na rundunar soji ta 22 da ke Ilorin, Captain Stephen Nwankwo, a wata sanarwa ne ya tabbatar da faruwar lamarin ya kuma ce, ɗaya daga cikin jami’an da suke kula da gandun dajin yankin...
Aƙalla mutum biyar ne suka rasu lokacin da ’yan bindiga suka kai hari wani Masallaci, yayin da ake tsaka da sallar Asuba a garin Yandoto da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe a Jihar Zamfara. Harin ya faru ne da safiyar ranar Juma’a, lamarin da ya girgiza al’ummar yankin. ‘Da albashin aikin masinja na fara kasuwancin Sahad Store’ Ganduje ya gindaya wa Kwankwaso sharadin shiga APC Shaidu sun ce maharan sun kutsa cikin Masallacin inda suka fara harbi ba tare da ƙaƙƙautawa ba, inda suka kashe mutum biyar nan take tare da jikkata wasu da dama. Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce maharan sun kuma yi awon gaba da wasu Masallata. Ya bayyana lamarin a matsayin “rashin...
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Mallakar makamashin nukiliya hakkin Iran ne, kuma tattaunawa da Amurka ya kai ga toshasshiyar hanya Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya gabatar da jawabinsa ta gidan talabijin, inda ya yi jawabi kan batutuwan cikin gida da na shiyya da kuma kasa da kasa. Jagoran ya dauki matakin wuce gona da iri da yahudawan sahayaniyya suka yi wa kasar Iran da nufin kifar da gwamnati, amma hadin kan al’ummar kasar ya hana hakan. Dangane da batun makamashin nukiliya kuwa, ya jaddada cewa Iran ba za ta yi watsi da haƙƙinta ba, yana mai nuni da mahimmancin makamashin nukiliya a fagage daban-daban. Dangane da tattaunawar da aka yi da Amurka,...
Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce ba su da matsala da yunkurin da aka ce tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso na yi na komawa jam’iyyar. Sai dai Ganduje ya ce suna da sharadin da dole sai Kwankwason ya amince da shi kafin ya shiga jam’iyyar. Aminiya ta rawaito yadda majijoyi masu tushe suka tabbatar da cewa tuni Kwankwaso ya fara tattaunawa da shugaban APC na kasa, Nentawe Yilwatda, a kan batun komawar. Kwankwaso ya fara tattaunawa da Nentawe kan maganar komawa APC Sauya Sheƙa: Kwankwaso ya gindaya sharuɗa kafin sake komawa APC Amma a cikin wata tattaunawarsa da Sashen Hausa na BBC, ranar Juma’a Ganduje ya ce jam’iyyar tana da dokoki da sharudda,...
Magajin garin Landan ya caccaki shugaban Amurka Trump, yana mai cewa shi mai nuna wariyar al’umma ce tare da kyamar musulmi Magajin garin Landan Sadiq Khan ya bayyana shugaban Amurka Donald Trump a matsayin “mai nuna wariyar al’umma kuma mai kyamar musulmi,” bayan da Trump ya zarge shi da neman aiwatar da shari’ar Musulunci a babban birnin Birtaniya. Khan ya shaida wa tashar Sky News cewa: “Yana ganin Trump a matsayin mai nuna wariyar al’umma, mai dabi’ar bunsuro, mai son zuciya, kuma mai kyamar musulmi.” Ya yi nuni da cewa, Landan ce ta farko a cikin alamomi da dama, kamar zuba hannun jari na kasashen waje, ya kuma jaddada cewa “yana matukar alfahari da cewa Landan ce birni mafi girma...
A yau Juma’a Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo zai mika sandar sarauta ga sabon Olubadan na Ibadan na 44, Oba Rashid Adewolu Ladoja. Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu da tsohon mataimakin Shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar za su halarci wannan gagarumin biki da aka shirya yi a Ibadan babban birnin Jihar Oyo. Bikin da ba a taba yin irinsa a Ibadan ba Shugaban Hadaddiyar Kungiyar Dattawa ’Yan asalin Ibadan (CCII), Cif Ajeniyi Ajewole ya ce, dukkan attajirai ’yan asalin Ibadan an dora masu haraji daga Naira miliyan 10 zuwa sama a matsayin gudunmawarsu ga wannan biki da aka fara da addu’ar rokon Allah a ranar Litinin da ta gabata. Ya ce, “mun kammala shirin yin bukukuwan nada...
Tashar ta jihar Legas na da natukar mahimmanci a tsarin jigilar shofar da kaya a kasar nan wadda kuma ta kasance a kan gaba wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin kasar nan. A hirar da da manema labarai Manajin Darakta na TTP Jama Onwubuariri ya bayyana cewa, wasu daga cikin nasarorin da aka samu a bangaren na TTP tun lokacin da aka faro sun hada da, sanya ido kan sama da manyan motocin miliyan uku da ke shiga cikin Tashoshin musamman bisa nufin rage cunkoson da kuma sake fitarsu, daga cikin Tashoshin a kan lokaci Ya sanar da cewa, kirkiro da tsarin biyan kudade kan lokaci na shigar motocin cikin Tashoshin hakan ya taimaka matuka, wanda kuma bisa hadakar da...
Alkaluma sun nuna cewa, a yankin Arewa Maso Gabas, kalubalen rashin tsaro ya dakatar da akalla yara miliyan 20, daga zuwa Makarantar Boko tare tare da kuma yadda hare-haren, suka lalata Makarantun Boko da dama da ke a yankin, wanda hakan ya janyo gagarumar tazara a tsakain yankin da kuma Kudancin kasar, tare da kuma wasu lamuran da suka shafi al’ada a fadin kasar, wanda ya kai kaso 15. Misali, yankin Arewa Maso Gabas, kacal irin wadannan hare-haren babu kakkautawa da mahara ke kai wa ya dakatar da yara miliyan biyu daga zuwa Makaranta inda hare-haren suka lalata gine-genen Makarantu da dama hakan kuma ya kara haifar da karancin Malaman. Malamai 915,913 kacal ne a matakin karatun Firamare ke koyar...
Kwararan bayanai na nuni da cewa tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya fara tattaunawa da Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, kan shirin komawa jam’iyyar. Majiyoyi daga cikin APC a Kano sun bayyana cewa Kwankwaso ya rubuta wasiƙa zuwa sakatariyar jam’iyyar ta ƙasa a Abuja, yana sanar da aniyarsa ta komawa jam’iyyar. An rufe wurin haƙar zinare a Kebbi Sauya Sheƙa: Kwankwaso ya gindaya sharuɗa kafin sake komawa APC Sai dai Aminiya ba ta iya tabbatar da hakan ba ya zuwa lokacin hada wannan rahoton. Wata majiya daga sakatariyar APC ta ƙasa kuma ta tabbatar da cewa ana ci gaba da tattaunawa tsakanin Kwankwaso da Farfesa Nentawe kan sauya shekar, kuma maganar ta yi nisa...
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Cin guba ta hanyar abinci (food poisoning) wata cuta ce da ke faruwa idan mutum ya ci abinci ko ya sha abin sha da ya gurɓace. Gurɓacewar abincin na iya fitowa daga ƙwayoyin cuta kamar Salmonella, E. coli, ko Listeria, ko kuma daga ƙwayoyin cutar virus, ƙwari (parasites), ko sinadarai masu guba. Alamomin cutar sun haɗa da ciwon ciki, amai, zazzabi, gudawa, da rashin jin daɗin jiki. A wasu lokuta masu tsanani, cutar na iya kai mutum asibiti ko ta yi barazana ga rayuwa, musamman ga yara ƙanana, mata masu ciki, tsofaffi, da masu raunin garkuwar jiki. NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Suke Sa Dalibai Cin NECO Fiye da WAEC DAGA LARABA:...
Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na shekarar 2025 na Naira biliyan 75 na kasafin kuɗin jihar da ƙananan hukumomi. An amince da kasafin kuɗin ya zama doka ne a yayin zaman majalisar wanda mataimakin Shugaban Majalisar Hon. Sani Isiya ya jagoranta. Ana zargin mai shagon kemis da ya yi wa ’yar shekara 14 fyaɗe a Filato An kashe ’ya’yan magoya bayan Gwamna Zulum Matakin ya biyo bayan amincewa da rahoton kwamitin kasafin kuɗi na Majalisar wanda Hon Ibrahim Hamza Adamu ya gabatar. Ƙarin kasafin kuɗin da aka amince da shi ya ƙunshi Naira biliyan 58 na Gwamnatin Jiha da kuma Naira biliyan 17 na Ƙananan Hukumomi 27, wanda ya ƙunshi kashe kuɗaɗe na yau da...
Har kullum Sin tana nacewa shawarwari, da tuntubar juna a matsayin muhimman matakan kyautata hadin gwiwa dake share fagen inganta cudanya. Tare da hakan, Sin na fatan Amurka za ta kaucewa kokarin dakile ci gabanta. Kuma duk wasu matakai na matsin lamba daga bangare guda kan kasar Sin, ba za su taba yin nasara ba, kamar dai yadda muka gani a baya. Don haka, a wannan gaba da ake ta samun karin sakamakon kyautata muamala da gudanar da shawarwari, kamata ya yi bangaren Amurka ya kauracewa kakaba shingen cinikayya, wanda ka iya gurgunta nasarorin da aka riga aka cimma. (Saminu Alhassan) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na...
Dangin wata yarinya ’yar shekara 14 a unguwar Gangare da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato, sun nemi a bi musu haƙƙi bisa zargin fyaɗen da wani mazaunin unguwar ya yi mata. Bayanai sun ce tun farko an cafke mutumin da ake zargi, Ibrahim Rawi, wanda da fi sani da Baban Siyama, amma daga bisani aka sake shi bayan wasu dattawan unguwar sun sa baki. Matashi ya kashe kakanninsa saboda abinci a Kano An kashe ’ya’yan magoya bayan Gwamna Zulum Budurwar da abin ya faru da ita da ke koyon sana’a a wajen mutumin da ake zargi, ta ce lamarin ya faru ne tsakanin ƙarfe 7 zuwa 8 na daren ranar Lahadi yayin da ake ruwan sama. A cewarta:...
Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta kama wani matashi ɗan shekara 30 mai suna Mutawakilu Ibrahim da laifin daɓa wa kakanninsa wuwa har lahira bayan wata taƙaddama kan abinci a Ƙofar Dawanau Ƙuarters da ke cikin birnin Kano. A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ta ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis, 25 ga watan Satumba, 2025 da misalin ƙarfe 9:30 na safe. An kashe ’ya’yan magoya bayan Gwamna Zulum Zan kare muradun Yarbawa idan aka zaɓe ni a 2027 — Atiku Rahotannin ’yan sanda sun nuna cewa, wanda ake zargin ya yi zazzafar taƙaddama da kakansa, Muhammad Dansokoto mai shekara 75 da kuma kakarsa, Hadiza Tasidi...
Daga nan sai ya jaddada aniyar Sin, ta ci gaba da goyon bayan matsayi da ikon MDD, tare da mara baya ga sassan kasa da kasa wajen cimma nasarar amfani da dandalin MDDr a matsayin fagen karfafa shawarwari da hadin gwiwa, da tsare-tsare da aiwatar da matakai yadda ya kamata. Haka kuma, a yayin zantawarsa da shugabar taron MDD karo 80 Annalena Baerbock, a gefen babban taron muhawarar majalissar dake gudana a halin yanzu, firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ce Sin na goyon bayan gina MDD mai karin inganci da hangen nesa, ta hanyar gudanar da sauye-sauyen kyautata karko da nagartar ayyukanta. Ya kuma bayyana kakkarfan goyon bayan Sin ga ikon MDD, da rawar da take takawa a...
Ba madatsar ruwa ta Dashimen kadai ce ta ba da damar noma amfanin gona a cikin yankin hamada ba. A cikin shekaru goma da suka gabata, yawan madatsan ruwa da aka gina ko gyara a yankin kwarin Tarim ya kai fiye da 120, wadanda suka hada rassan kogin Tarim 144, kuma hakan ya samar da babban tsarin ban ruwa a wurin, har ya mai da sassan hamada su zama gonaki. A cikin hamadar da ke gundumar Qiemo, ana ta kara samun dausayi, inda masarar da malam Li Wenbin ya shuka ta kusan nuna. A cikin shekaru goma da suka gabata, karuwar gonaki a jihar Xinjiang ta kai fiye da muraba’in kilomita 8000, wanda ya sa jihar zamanto yankin da ya...
Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ya shawarci matasa da ’yan siyasa masu tasowa da su fahimci cewa harkar siyasa ba ta tafiya da rowa, illa juriya da sadaukarwa da biyayya. Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin da yake rantsar da sabon Alƙalin alƙalai na jihar (Grand Khadi) tare da wasu Masu Ba da Shawara na Musamman, Memba na dindindin a hukumar SUBEB, da kuma Sabbin sakararorin dindindin guda 13 a wani taro da aka gudanar a babban ɗakin taro na gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu. An gurfanar da malamai kan zargin lalata da ɗalibarsu a Zariya Hajjin 2025: Mun samu nasarori a Yobe — Mai Aliyu Biriri A jawabinsa, Gwamna Buni ya ce matasa da...
An gurfanar da wasu malamai biyu na wata makaranta ta Zariya Children School da ke yankin GRA Zariya, a gaban kotun majistare da ke Tudun Wada bisa zargin lalata wata ɗalibar makarantar mai shekaru 11. Jami’in da ke gabatar da ƙara a gaban kotun, ASC Mustapha Abdulkadir, ya ce malamai biyu tare da wasu uku da suka tsere, na fuskantar tuhuma kan laifin aikata lalata, wanda ya saba wa sashi na 259 na kundin laifukan Jihar Kaduna na shekarar 2017. An ceto mutum 5 bayan gini ya rufta da su a Legas Gwamnatin Katsina ta kori ma’aikata da malaman makaranta na bogi 3,488 Ya bayyana cewa, a ranar 11 ga watan Satumba wani mai suna Yahaya Aliyu, mazaunin Tudun Jukun...
Shugaban Hukumar Alhazzan Jihar Yobe, Alhaji Mai Aliyu Usman Biriri ya bayyana cewar sun gudanar da aikin Hajjin 2025 cikin nasara da kwanciyar hankali. Mai Aliyu ya bayyana hakan ne ranar Laraba a tattaunawarsa da manema labarai a babban ɗakin taron Hukumar da ke garin Damaturu dangane da yadda suka gudanar da aikin hajjin bara. An ceto mutum 5 bayan gini ya rufta da su a Legas Muhimman abubuwa 7 da Najeriya ta fada yayin jawabinta a taron MDD Shugaban ya ƙara da cewa, duk da cewar sakamakon yanayin yadda lamurran rayuwa suke ga al’umma wadda ya kai da ba su samu damar cika yawan kujerun da aka bai wa Jihar ba, amma duk da haka kusan mahajjata 1098 ne suka...
Ya ce zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya zai tabbata ne kawai idan aka tabbatar da adalci. Shugaban ya jaddada irin gyare-gyaren tattalin arziƙin Nijeriya, ciki har da cire tallafin man fetur da sauya dokokin musayar kuɗi. Ya ce matakan suna da tsauri, amma dole ne a ɗauke su domin samar da ci gaba mai ɗorewa. A kan tsaro, Tinubu ya ce yaƙin da ta’addanci ba wai da bindiga kaɗai ake cin nasara ba, sai da ra’ayoyi da ɗabi’u waɗanda ke haɗa al’umma. Ya kuma jaddada aniyar Nijeriya ga zaman lafiya, ci gaba, da kare haƙƙin ɗan Adam, inda ya yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta yi canje-canjen da za a iya gani, tare da gargaɗin cewa idan...