Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori
Published: 11th, November 2025 GMT
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya jaddada kudirin gwamnatin sa na ci gaba da bunkasa hanyoyin sufuri a fadin jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya kaddamar da wani muhimmin aikin gina hanyoyi a karamar hukumar Mallam Madori.
Yayin taron kaddamarwar, Gwamna Namadi ya bayyana cewa aikin yana cikin shirin “Gwamnati da Jama’a” wanda ke karfafa al’umma, rage matsalolin sufuri da kuma karfafa harkokin kasuwanci.
Ya ce shirin ya kunshi gina manyan hanyoyi guda shida a sassan jihar, masu tsawon kilomita 179 gaba daya, a kan kudin da ya haura Naira Biliyan 81.
Hanyoyin sun hada da Mallam Madori zuwa Gari Uku zuwa Kanya Babba zuwa Malorin Kasim, ta ratsa ta Abori Sumburtu, har zuwa Diginsa, mai tsawon kilomita talatin da hudu da rabi.
Sai kuma hanyar Arbus zuwa Girbobo zuwa Garin Bukar mai nisan kilomita talatin da uku da rabi.
Kazalika akwai hanyar Dundubus zuwa Yanjaji zuwa Wangara mai tsawon kimanin kilomita goma sha bakwai.
Akwai kuma hanyar Jahun zuwa Takalafiya zuwa Zareku zuwa Kafin Hausa da reshe daga Takalafiya zuwa Dangyatum mai kilomita talatin da takwas.
Da hanyar Kukayasku zuwa Malamaba zuwa Katuka zuwa Garin Kwalandi mai nisan kilomita talatin da hudu da rabi.
Sai cikon ta shidda wacce ta tashi daga Farun Daba zuwa Maitsani zuwa Baauzini zuwa Kafin Chiroma zuwa Gallu Babba zuwa Gallu Karama ta kai ga Karkarna Bypass mai nisan kilomita goma sha uku.
Gwamnan ya bayyana cewa tuni an yi kashi 35 cikin 100 aikin, yana mai fatan cewa za a gama shi cikin shekara guda, kafin wa’adin watanni 18.
Ya tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da baiwa ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da samar da ayyukan yi muhimmanci a karkashin Manufofi 12 na Gwamnati don Cigaban Jigawa.
Ya kuma gode wa Gwamnatin Tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa tallafi da daidaiton manufofi.
A yayin ziyarar, Gwamna Namadi ya kuma kaddamar da sabon masallaci da aka gina a Garin Gabas, wanda shugaban karamar hukuma ya tallafa wajen ginawa.
Shugabannin al’umma sun mika wa Gwamnan kundin bukatun jama’a a matsayin wani bangare na tsarin mulkin jin ra’ayin al’umma.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Kebbi ya gargaɗi manoma da makiyaya kan su zauna lafiya ko su fuskanci hukunci
Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya gargaɗi manoma da makiyaya a Ƙaramar Hukumar Arewa, da su daina faɗa tare da zama lafiya, ko kuma su fuskanci hukunci a kotu.
Gwamnan, ya yi wannan gargaɗi ne yayin da ya ziyarci mutanen da suka rasa muhallansu sakamakon rikici, waɗanda yanzu ke zaune a harabar sakatariyar Ƙaramar Hukumar Arewa da ke Kangiwa.
Ya kamata duk ɗan Najeriya ya damu da barazanar Trump– Jigon APC Mataimakin Shugaban Majalisar Kebbi ya kuɓuta daga hannun ’yan bindiga“Na zo ne don jajanta wa iyalan waɗanda suka rasa rayukansu a dalilin wannan rikici, amma dole ne mutane su daina ɗaukar doka a hannunsu,” in ji shi.
Gwamnan, ya ce gwamnati ta fara bincike don gano musabbabin rikicin, inda ya ƙara da cewa an riga an kama wasu, kuma kotu za ta hukunta masu laifi.
Ya kuma sanar da bayar da tallafin Naira miliyan 150 ga iyalan waɗanda lamarin abin ya shafa a ƙauyukan Fulani, Zabarmawa da Arewa.
“Babu wani dalili da zai sa rikici ya shiga tsakaninsu, tun da kun shafe sama da shekaru 100 kuna rayuwa tare cikin zaman lafiya,” in ji shi.
Gwamnan, ya kuma yi alƙawarin neman taimakon Gwamnatin Tarayya domin tallafa wa waɗanda abin ya shafa, tare da yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu na tabbatar da zaman lafiya a yankin.