’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su
Published: 21st, November 2025 GMT
’Yan bindigar da suka yi garkuwa da masu ibada a cocin Christ Apostolic Church da ke Eruku, a jihar Kwara, sun nemi Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansar kowanne mutum da suka kama.
A cewar Faston cocin, Lawrence Bamidele, tsakanin mutane 30 zuwa 35 aka yi garkuwa da su a daren Talata lokacin da aka kai musu mummunan hari suna tsaka da ibada a cocin.
Majiyoyi daga iyalai da shugabannin al’umma sun tabbatar a ranar Alhamis cewa masu garkuwar sun fara kiran ’yan uwan waɗanda aka sace ta hanyar amfani da wayoyinsu.
Sakataren cocin, Josiah Agbabiaka, ya ce tuni aka fara tuntubar wasu daga cikin dangin wadanda aka sace din.
Ya ce, “Gaskiya ne cewa ’yan bindigar sun fara kiran ’yan uwa ta amfani da wayoyin waɗanda aka sace don neman kudin fansa,” in ji Agbabiaka.
“Abin da aka shaida mana shi ne sun raba waɗanda aka sace gida-gida. Rukunin farko na mutane 11 an nemi su biya Naira miliyan 100 kowanne.”
Basaraken gargajiya na yankin, Olori Eta, Cif Olusegun Olukotun, wanda ’yan uwansa huɗu na cikin waɗanda aka sace, ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa masu garkuwar suna kiran dangin wadanda aka sace daya bayan daya.
“’Yan bindigar sun fara kiran wasu suna neman Naira miliyan 100 kan kowanne mutum. Sun ce sun raba waɗanda aka sace gida-gida, kuma suna kiran danginsu,” in ji shi.
Olukotun ya ce yana cikin cocin tare da ’yan uwansa biyar lokacin harin, inda ya ce ya tsere ta taga yayin da sauran aka tafi da su.
Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sanda ta Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta ce rundunar ba ta samu wani rahoto a hukumance ba kan neman kudin fansar.
“Ba mu da masaniya kan wani neman kudin fansa ko tuntubar iyalan waɗanda aka sace,” in ji ta a ranar Alhamis.
“Dakarunmu na musamman tare da sojoji da sauran jami’an tsaro suna kan aiki don ceto waɗanda aka yi garkuwar da su.”
Ejire-Adeyemi ta ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adekimi Ojo, ya roƙi al’umma da iyalan waɗanda aka sace da su bayar da bayanan da za su taimaka wa jami’an tsaro wajen aikin ceto mutanen kuma a kan lokaci.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Harin cocin Kwara waɗanda aka sace yan bindigar Yan bindigar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi
Gwamnan Taraba, Agbu Kefas ya sanar da dakatar da sauya sheƙa daga jam’iyyarsa ta PDP zuwa APC a dalilin sace ɗalibai mata ’yan sakandire da aka yi a Jihar Kebbi.
Gwamnan ya ce zai ci gaba da tattaunawa da kuma nazari kan lokacin da ya fi dacewa ya sauya sheƙar tare da magoya bayansa.
Mutane 7 sun mutu a hatsarin mota a Jigawa Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai mata a KebbiAminiya ta ruwaito cewa, da sanyin safiyar Litinin, 17 ga watan Nuwambar 2025, mahara suka shiga a makarantar sakandare ta ’yan mata da ke garin Maga a Jihar Kebbi, inda bayanai ke nuni da cewa sun yi awon gaba da ɗalibai 25 tare da halaka mataimakin shugaban makarantar da wani maigadi kana suka jikkatar da dama.
Sai dai gwamnatin Najeriya ta bayyana tsananin damuwa kan harin, inda ta ce ta bai wa jami’an tsaro umarnin gano da ceto ɗaliban cikin gaggawa.
Cikin wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai, Muhammad Idris ya fitar, ya ce gwamnati za ta tabbata an kamo waɗanda suka kai harin domin su fuskanci hukunci.
Ya ƙara da cewa gwamnati na tare da iyaye da ’yan uwan waɗanda abin ya shafa, tare da jaddada cewa za a yi duk wani abu mai yiyuwa domin ganin yaran sun koma gida cikin aminci.
Ita ma ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International, ta yi kakkausar suka kan sabon harin, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici wanda ta ce ya tabbatar da gazawar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan kasa ballantana kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga.