Aminiya:
2025-11-21@20:20:23 GMT

Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa

Published: 21st, November 2025 GMT

Majalisar Dokokin Jihar Kano, ta wanke Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano da aka dakatar, Alhaji Naziru Yau, daga dukkanin zarge-zargen da aka masa.

Wannan ya ba shi damar komawa bakin aikinsa da shugabancin Ƙaramar Hukumar Rano.

An kama Faston da ake zargi da yi wa mambobin cocinsa 3 fyade ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su

An dakatar da Yauyayin da ake bincike a kansa.

Bayan sanar da dawo da shi kan kujerunsa, dubban magoya bayansa ne suka tarbe shi da murna a kan iyakar Rano da Bunkure.

Daga nan ya wuce zuwa fadar Sarkin Rano, Muhammad Isa Umaru, wanda ya yi masa addu’a kafin ya sake komawa ofis ɗinsa da ke sakateriyar Ƙaramar Hukumar Rano.

Da yake yi wa ma’aikata da magoya bayansa jawabi, Yau, ya gode wa Allah da Ya tsare masa mutuncinsa.

Sannan ya gode wa Majalisar Dokokin jihar da ta wanke shi.

Ya yi godiya ga Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Gwamna Abba Kabir Yusuf, shugabannin NNPP da sauran masu ruwa da tsaki da suka taimaka wajen dawo da shi kan kujerarsa.

Tun farko an dakatar da shi ne bayan kwamitin karɓar ƙorafe-ƙorafe na majalisar ya miƙa rahoton wucin-gadi.

Rahoton ya zarge shi da aikata ba daidai ba, cin zarafin ofishinsa, karkatar da dukiyar jama’a da kuma aikata rashin gaskiya wajen sarrafa kuɗaɗen gwamnati.

Sauran zarge-zargen sun haɗa da haifar da rikici tsakanin shugabannin siyasa, sayar da taki sama da farashin da gwamnati ta ƙayyade, da kuma rashin bayyana gaskiya wajen karɓar kuɗaɗen haraji na kasuwanni.

Haka kuma an zarge shi da sayar da rumfunan kasuwa ba bisa ƙa’ida ba.

Yanzu da an wanke shi daga dukkanin zarge-zargen, ya koma bakin aikinsa a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Rano.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Rano Yau Zarge zarge Ƙaramar Hukumar Rano

এছাড়াও পড়ুন:

Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya

Ƙaramin kwamitin majalisar dokokin Amurka kan harkokin kasashen Afirka ya yi wani zama kan batun zargin kisan kiyashin da ake yi wa Kiristoci a Nijeriya da batun yadda Shugaba Donald Trump ya ayyana kasar a matsayin “wadda Amurka ke nuna damuwa a kanta kan walwalar addini,” sai dai kawunan mambobin majalisar sun rarrabu a kan batun na Nijeriya.

Zaman, wanda aka yi a Majalisar Dokokin Amurka da ke birnin Washington a ranar Alhamis ya ƙunshi ’yan majalisa da masu kare hakkin dan’adam da kuma wasu kungiyoyin fararen hula.

An shafe lokaci ana lugudan laɓɓa da musayar yawu tsakanin mambobin majalisar da sauran waɗanda suka halarci zaman, wanda aka kuma yada shi kai-tsaye ta intanet.

Masu magana a wajen sun haɗa da Babban Jami’i na Cibiyar Harkokin Amurka Jonathan Pratt da Mataimakin Sakataren Cibiyar Dimokuradiyya, Hakkokin Dan’adam da Ƙwadago, Jacob McGee.

Sai kuma Daraktar Cibiyar ‘Yancin Addini, Ms Nina Shea; da Bishop Wilfred Anagbe na Cocin Katolika ta Makurdin Nijeriya; da Ms Oge Onubogu ta Cibiyar Dabaru da Karatun Ilimin Ƙasa da Ƙasa, waɗanda suka sha tambayoyi daga ‘yan majalisar.

Yayin da wasu mambobin suka goyi bayan ayyana Nijeriya a matsayin “kasar da Amurka ke nuna damuwa a kanta kan walwalar addini” da daukar mataki kan Nijeriya lokacin da suke jawabi, akwai wasu daga cikin mambobin majalisar da suka bukaci a sake duba matsayin da Amurkan ta ɗauka, inda suka ce abubuwan da ke faruwa suna da sarƙaƙiya kuma suna bukatar a duba su da idon basira.

Ko da yake Shugaban Kwamitin, Chris Smith wanda ɗan jam’iyya mai mulki ta Republican ne kuma yana wakiltar Jihar New Jersey, yayin da yake jawabin bude taron ya bayyana cewa zaman yana da muhimmancin gaske, don Amurka ba za ta zuba ido kan abubuwan da suke faruwa a Nijeriya ba, kuma hakan ne ya sa yake yawan kira kan cewa akwai bukatar a dauki mataki kan ƙasar.

Sai dai wasu ’yan majalisar dokokin Amurka ba su goyi bayan matsayin Shugaba Trump kan cewa ana kisan Kiristoci a Nijeriya ba.

’Yar majalisar wakilai ’yar jam’iyyar adawa ta Democrat Pramila Jayapal ta ce ba ta goyon bayan daukar matakin soji a kan Nijeriya, inda ta bayyana cewa Nijeriya tana da matukar muhimmanci ga Amurka da ƙasashen Afirka.

Ta ce kashe-kashen da ke faruwa a Nijeriya ba Kiristoci kawai yake shafa ba, inda ta ce ana kashe hatta mabiya sauran addinai a kasar.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargi: Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba
  • Gwamnatin Kwara ta rufe makarantu a kananan hukumomi 4 saboda matsalar tsaro
  • Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  • An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari