Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta tabbatar da bada cikakken goyon bayanta ga Kwalejin Aikin Noma ta Gwamnatin Tarayya da ke Kirikasamma.

Gwamna Umar Namadi ya bayar da wannan tabbaci ne lokacin da ya karɓi tawagar gudanarwar kwalejin ta farko, ƙarƙashin jagorancin shugabanta, Dr. Muhammad Yusha’u Gwaram, yayin ziyarar girmamawa da suka kai Gidan Gwamnati da ke Dutse.

Ya taya shugaban kwalejin da tawagarsa murna, inda ya bayyana nadin nasu a matsayin tarihi kuma mai matuƙar muhimmanci.

Malam Umar Namadi ya ƙara da cewa kafa sabuwar cibiyar ilimi aiki ne babba, yana mai bayyana tabbacin cewa  mutanen da aka zaba don fara gudanar da kwalejin za su taka rawar gani.

“Kafa sabuwar cibiyar ilimi ba abu ba ne mai sauƙi. Kun shiga tarihin wannan kwaleji, wacce idan ta yi nasara, za a tuna da ku cikin alheri; idan ta gaza kuma, babu shakka hakan zai shafe ku. Amma ina da tabbaci, ganin irin mutanen da ke cikin wannan tawaga, cewa kwalejin ta fara da ƙafar dama,” in ji shi.

Namadi ya bayyana godiyarsa ga Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa amincewa da dokokin da suka kafa Kwalejin Noma ta Tarayya a Kirikasamma da Kwalejin Ilimi ta Tarayya da ke Birnin Kudu, inda ya bayyana cewa Jigawa na kan hanyar samun wata cibiyar tarayya ta uku bayan tattaunawar da ya yi da shugaban ƙasan.

Gwamna Namadi ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba da cikakken goyon baya ga tawagar gudanarwar.

 

“Za mu yi duk mai yiwuwa don tabbatar da nasarar fara aiki a kwalejin, kuna da cikakken goyon bayanmu, mun yi sa’a sosai da samun Dr. Gwaram a matsayin jagoran wannan cibiyar, ƙwararren masani a fannin noma, gogaggen mai gudanarwa, kuma ɗan asalin Jigawa mai kishin ƙasa.”

Ya yaba wa Ministan Noma, Ministan Ilimi, da ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Mazabar Birniwa/Guri/Kirikasamma, Alhaji Fulata, kan rawar da suka taka wajen ganin an kafa sabuwar kwalejin.

Haka kuma ya jinjinawa shugaban kwalejin da Kwamishinan Ilimi na manyan makarantu bisa jajircewarsu.

Tunda farko, shugaban kwalejin, Dr. Muhammad Yusha’u Gwaram, ya bayyana godiyarsa ga gwamnatin jihar bisa goyon bayanta, tare da jaddada cewa kwalejin ta shirya fara aiki nan take.

A cewarsa, kwalejin za ta kasance cibiya ta musamman da za a koyar da ingantattun hanyoyin noma na zamani.

Ya bayyana cewa sun shirya horas da manoma da kuma jawo hukumomin da suka dace zuwa Jihar Jigawa.

Ya ce sun fara tattaunawa da hukumomin da ke da alhakin rajista da tsari kamar NBTE da sauran da ake buƙata don fara aiki.

Ya yaba da irin  ƙoƙarin da aka yi wanda ya kai ga amincewa da kafa cibiyar, yana mai jaddada yawan tattaunawar da aka yi da hukumomin tarayya, masu tsara doka, da masu ruwa da tsaki, tare da tabbatar wa gwamna cewa tawagarsu za ta yi aiki tukuru wajen cimma nasara kwalejin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Cibiyar Ilimi Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 

Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi, ya nemi ƙarin bayani kan dalilin ɗauke sojojin da ke gadin makarantar GGCSS Maga, gabanin harin da ’yan bindiga suka kai tare da sace ɗalibai 25.

Gwamnan, ya ce gwamnati ta riga ta sanar da hukumomin tsaro game da yiwuwar kai hari, amma sojojin suka bar makarantar da misalin ƙarfe 3 na dare.

Zargi: Majalisar Kano ta dawo da shugaban ƙaramar hukumar Rano kan kujerarsa Gwamnatin Neja ta zargi makarantar da aka sace wa dalibai da kin bin umarninta

“An tura sojoji, amma sun bar makarantar da misalin ƙarfe 3 na dare, sannan ƙarfe 3:45 harin ya faru. Wa ya bayar da izinin su bar makarantar a wannan lokaci mai muhimmanci?” in ji Idris.

Ya ce bayan barin makarantar da sojoji suka yi ƙasa da awa guda ’yan bindiga suka kai hari.

Ya ce barin makarantar da sojojin suka yi, ya saɓa wa alƙawuran da aka yi na ƙarfafa tsaro a makarantu da ke kan iyakar jihar.

Idris, ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya da ta jihar na aiki tuƙuru don ceto ɗaliban da aka sace.

Gwamnan, ya bayyana cewa an umarci malaman addini da su yi addu’a domin samun zaman lafiya da kuɓutar da waɗanda aka sace.

Idris, ya ce abin da ya faru na nuna cewa akwai maƙiya da ke ƙoƙarin kawo cikas ga ci gaban jihar.

A yayin ziyarar nuna goyon baya, Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce abin da ya faru abin damuwa ne, musamman ma a lokacin da Kebbi ke samun ci gaba mai kyau.

Ya ƙara da cewa duk wani yunƙuri na daƙile ci gaban jihar ba zai yi nasara ba, kuma ya shawarci gwamnan da ya dage.

Ajaero ya ce, “Wannan kawo cikas ne, amma duk wani yunƙuri na daƙile ci gaban jihar ba zai yi nasara ba. Muna tare da ku.”

A halin yanzu, rundunar sojin ƙasa ta fara bincike kan dalilin da ya sa sojojin da aka tura makarantar suka bar wajen aiki kafin aukuwar harin.

Majiyoyin tsaro sun ce a yanzu haka an fara binciken wasu manyan jami’ai kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP
  • IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka
  • Na sha alwashin kafa tarihi a Camp Nou — Lamine Yamal
  • Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
  • Cibiyar fasaha ta kaddamar da shirin bunkasa tattalin arzikin ’yan kasuwa mata a Jihohi 3