Aminiya:
2025-11-22@08:55:19 GMT

Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN

Published: 22nd, November 2025 GMT

Yawan ɗaliban da aka sace a makarantar Sakandaren St. Mary’s da ke Jihar Neja ya kai 215 da kuma ma’aikata 12 a cewar Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN).

Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) Reshen Jihar Neja, Rabaran Bulus Dauwa Yohanna, ya ce mutum 227 aka sace a makarantar, ɗalibai 215 da kuma malamai 15.

A safiyar Juma’a ne ’yan bindiga suka kutsa makarantar da ke yankin Papiri da ke Karamar Hukumar Agwara ta jihar Neja suka yi awon gaba da su.

Da yake jawabi bayan ziyartar makarantar, ya bayyana cewa, “Na gana da iyayen ɗaliban kuma mun tabbatar musu cewa muna aiki tare da gwamnati da jami’an tsaro domin ganin an ceto yaran.

Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya

“Alƙaluman da aka tattara sun nuna yara 215 da malamai 12 ne ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a garin.

“Akwai yaran da suka tsere a lokacin da aka kai harin, kuma iyayen sun zo suka kwashe ’ya’yansu tunda an rufe makarantu,” in ji shi.

Aminiya ba ta iya tabbatar da alƙaluman ba, kuma hukumomi ba su fitar da nasu alƙaluman ba, zuwa lokacin da muka kammala wannan labari.

Wakilinmu ya gano cewa da misalin ƙarfe 2 na dare ne ’yan bindigar suka kai harin, inda daga bisani suka loda ɗaliban da malaman a cikin wata babbar mota da suka ƙwace a yankin.

Daga baya sun jefar da motar a hanya bayan da ya samu matsala, suka kora mutanen zuwa cikin daji.

An kai harin ne kwana huɗu bayan a ranar Litinin ’yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai 26 makarantar ’yan mata ta GGCSS da ke yankin Maga a Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu da ke Jihar Neja — ’yan bindigar na neman kuɗin fansa Naira miliyan 100 a kan ɗaliban.

Aminiya ta ruwaito cewar Gwamnatin Tarayya ta ba da umarnin rufe duk makarantunta na kwana guda 41 da ke faɗin ƙasar nan a sakamakon hare-haren.

Kafin nan gwamnatin jihar Katsina ya rufe ɗauƙacin makarantu, gwamnatin Filato ta rufe ɗauƙacin makarantun ƙananan sakandare, a yayin da gwamnatin Kwara ta rufe wasu makarantu 50 a wasu yankuna saboda tsaro, bayan sace Ɗaliban Makarantar Maga.

Gwamnatin Jihar Neja zargi Hukumomin Makarantar St. da rashin bin umarnin kada a bisa ga makarantar saboda rashin tsaro a yankin, amma hukumomin makarantar suka yi biris da umarnin gwamnatin suka yi gaban kansu wajen buɗe makarantar, lamarin da ya jefa rayuwar dalibai da malaman cikin haɗari.

Idan ba a manta ba, bayan harin Makarantar Maga, Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci Ministan Tsaro Bello Matawalle da ya koma Jihar Kebbi, jami’an tsaro kuma su tabbata sun ceto yaran cikin aminci.

SP Wasiu Abiodun, kakakin ’yan sanda na Jihar Neja, ya tabbatar da harin tare da cewa an tura jami’an tsaron haɗin gwiwa na musamman domin ceto ɗaliban da malamansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Ɗalibai Garkuwa Makaranta St Mary s Tsaro yara a makarantar

এছাড়াও পড়ুন:

Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, da ya koma jihar Kebbi da aiki sakamakon sace ɗalibai ’yan mata 25 da wasu ’yan bindiga suka yi a jihar.

Tinubu ya umurci Matawalle, wanda tsohon Gwamnan Jihar Zamfara ne, da ya zauna a Kebbi domin sa ido kan dukkan matakan tsaro da ake ɗauka domin kuɓutar da ɗaliban da aka sace.

Babu wani addini da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙyale — Fafaroma Za a aurar da marayu 200 a Zamfara

’Yan bindiga sun sace ɗalibai 25 a Makarantar Sakandiren Mata da ke garin Maga na Jihar Kebbi da misalin ƙarfe 4 na Asubahin ranar Litinin.

A cewar mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Bayo Onanuga wanda ya bayyana umarnin a cikin wata sanarwa da yammacin Alhamis, ana sa ran Matawalle zai isa Birnin Kebbi da safiyar Juma’a.

“Yana da ƙwarewa sosai wajen fuskantar ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara daga 2019 zuwa 2023,” in ji sanarwar.

“A ranar 26 ga watan Fabrairu, 2021, ’yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai mata 279 masu shekaru tsakanin 10 da 17 a makarantar kwana ta GGSSS Jangebe, Jihar Zamfara. ’Yan bindigar sun saki dukkan waɗanda suka yi garkuwar da su a ranar 2 ga watan Maris, 2021.”

Idan za a iya tunawa, Shugaba Tinubu ya dage tafiyarsa da aka tsara zuwa Johannesburg, Afirka ta Kudu, da Luanda a kasar Angola, domin ya jira ƙarin rahotannin tsaro kan satar daliban na Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada a cocin Eruku da ke jihar Kwara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • Gwamnatin Neja ta zargi makarantar da aka sace wa dalibai da kin bin umarninta
  • ’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja
  • Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai da Malamai a Jihar Neja
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Hamas Tayi Gargadi Game Da Kara Dagulewar Al’amura Bayan Harin Isra’ila A Gaza