Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Biliyan daya da miliyan dari uku domin gyara da inganta tsofaffin ayyukan wutar lantarki a fadin jihar.

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse.

A cewarsa, wannan mataki na daga cikin jajircewar gwamnatin Malam Umar Namadi wajen inganta samar da wutar lantarki da kuma bunkasa ci gaban al’umma musamman a yankunan karkara.

A cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai bayan zaman majalisar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, aikin na nuna kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da karin samun wutar lantarki, kara habakar tattalin arziki, da inganta rayuwar jama’a a birane da karkara.

Ya bayyana cewa, aikin zai kunshi samarwa da girka sabbin na’urorin bada wuta (transformers), hada garuruwa ta hanyar layin wuta na 33KV, da kuma maye gurbin turakun wuta da suka lalace a sassa daban-daban na jihar.

Sanarwar ta kara da cewa, garuruwan da za su amfana sun hada da Madaka a Gagarawa, Bosuwa a Maigatari, Mai Tsamiya da Unguwar Gawo a Sule-Tankarkar, Yandamo a Gumel, Farin a Dutse, Giginya a Gwaram, Kwanar Dindu zuwa Bulangu a Kafin Hausa, Kanya Babba a Babura da kuma Garki a Karamar Hukumar Garki.

Ya ce wannan aikin da aka yi na nuna jajircewar gwamnatin Namadi wajen samar da ci gaba mai dorewa da tabbatar da cewa kowace al’umma ta amfana da romon dimokuradiyya.

Alhaji Sagir ya kara da cewa, gwamnatin Namadi ta kuma amince da bayar da kwangilar gina rijiyoyin samar da ruwa da ke aiki da hasken rana domin sabbin gidaje na Danmodi Housing Estates.

Wadannan gidaje sun hada da na Birnin Kudu, Kafin Hausa, Kazaure, Ringim da kuma hanyar Nguru–Hadejia.

Kwamishinan ya bayyana cewa, kwangilar da ta kai fiye da Naira miliyan 378 tana nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen samar da muhimman abubuwan more rayuwa da ke kara ingancin zama da dorewar sabbin gidaje a fadin jihar.

Ya ce amincewar wannan aiki na nuna yadda gwamnatin Namadi ke aiwatar da tsare-tsaren ci gaba cikin tsari guda, wanda ya hada da gidaje, ruwa, da makamashi mai sabuntawa domin inganta rayuwar al’umma baki daya.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Wutar Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

APC Ta Yi Gangamin Karfafa Hadin Kan Mambobinta Bayan Kaddamar Da Aikin Titin Malam Madori

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanya da kudinta ya kai Naira Biliyan 14 a Karamar Hukumar Malam Madori, wanda ke nuna jajircewar gwamnatinsa wajen bunkasa ababen more rayuwa1 karkashin shirin sabunta kudurori na gwamnatin tarayya wato “Renewed Hope Agenda.”

A yayin taron kaddamarwar, an kuma gabatar da sabbin motoci ga shugabannin jam’iyyar APC guda takwas da masu tallata jam’iyyar a mazabar Arewa maso gabashin jihar, wanda Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya dauki nauyi.

Wannan mataki na da nufin karfafa hadin kai a jam’iyyar da kuma tallata hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadin jihar.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya yaba da jajircewar Sanata Ahmed Malam Madori na nuna biyayya, karamci, da sadaukarwa wajen ci gaban jam’iyyar APC. “Wannan babbar shaida ce ta jajircewar Sanata Malam Madori ga jam’iyyarmu”.

 

Haka kuma Gwamnan ya karfafa gwiwar sauran mambobi da su tallafa wa shirin ci gaba na Shugaba Tinubu karkashin ‘Renewed Hope Agenda.”

Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya bayyana cewa tallafin motocin na nufin bai wa mambobin jam’iyya damar yin ingantaccen aiki wajen tallata shirin ci gaba na Shugaban kasa da kuma Shirin Ci Gaba na Gwamna Namadi.

“Shugaba Tinubu da Gwamna Namadi sun kawo gagarumin ci gaba ga al’umma da ababen more rayuwa a Jigawa. An amince da kafa muhimman hukumomin tarayya, ciki har da Cibiyar Horar da ‘Yan Sanda a Kafin Hausa, Kwalejin Ilimi ta Tarayya a Malam Madori, da Kwalejin Noma ta Tarayya a Kirikasamma,” in ji shi.

Ya jaddada ayyukan Gwamna Namadi na baya-bayan nan, ciki har da aikin hanyar kilomita 47 da ke hada Hadejia–Garun Gabas, inganta asibitoci, da farfado da cibiyoyin lafiya na farko.

Sanata Malam Madori ya kara da jaddada hadin kan masu ruwa da tsaki na APC a mazabar Arewa maso gabashin Jigawa, wanda ya hada da ‘yan majalisar wakilai guda uku, ‘yan majalisar jihar guda tara, shugabannin kananan hukumomi takwas, da ‘yan majalisar kananan hukumomi 85

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Himmatu Wajen Inganta Harkokin Kiwon Lafiya a Jihar
  • Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Shirya Faɗaɗa Gonakin Shinkafar Jangwa Don Ƙara Samar da Shinkafa
  • Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
  • Gwamnatin Tarayya Ta Jinjinawa Gwamnan Jigawa Bisa Ayyukan Ci Gaban Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori
  • APC Ta Yi Gangamin Karfafa Hadin Kan Mambobinta Bayan Kaddamar Da Aikin Titin Malam Madori
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Asibitin Koyarwa Na RSUTH Ya Bada Fifiko Ga ‘Yan Asalin Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Asibitin Koyarwa Na RSUTH Ya Bada Fifiko Ga ‘Yan Asalin Jihar Yayin Daukar Ma’aikata
  • Kungiyar ‘Yan Dako Reshen Jigawa ta Kaddamar da Sabon Shugaba