Aminiya:
2025-12-13@13:27:11 GMT

DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu

Published: 12th, November 2025 GMT

Hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar wani matashi mai suna Innocent Chukwuemeka Onukwume, mai shekaru 27, bisa zargin kiran sojoji da su yi juyin mulki a Najeriya.

Hukumar dai ta shigar da ƙarar matashin ne cikin tuhuma shida a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja.

Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP PDP ta sha alwashin gudanar da babban taronta duk da umarnin kotu

An shigar da ƙarar ne mai lamba FHC/ABJ/CR/610/2025, dangane da wasu rubuce-rubuce da matashin ya wallafa a shafinsa na X a watan Oktoban 2025.

A cewar DSS, waɗannan rubuce-rubuce sun nemi a kifar da gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki tare da nuna goyon baya ga sojoji su karɓi mulki a ƙasar.

Lauyan DSS, A.M. Danalami, ya shigar da ƙarar a ranar Talata, inda aka bayyana cewa ayyukan wanda ake zargin sun saɓa da sashe na 46A(1) da 59(1) na Dokar Manyan Laifuka ta Ƙasa, da kuma Sashe na 24(1)(b) na Dokar Laifukan Intanet ta 2024 (wacce aka yi wa gyara).

Daga cikin kalaman da ake zargin ya wallafa akwai: “Ana buƙatar juyin mulki a Najeriya. A kawar da APC, a dakatar da gwamnatin Najeriya, a shiga kungiyar AES. Wannan ne kawai muke buƙata yanzu.”

Haka kuma, ana zargin ya rubuta cewa: “A karshe zai faru,  yak u ’yan Najeriya. Sojoji na buƙatar goyon bayanku yanzu! Su kaɗai ne za su iya ceton ƙasar nan. Wanda ke Aso Rock ya sayar da ƙasar nan ga Turawa, su ke sarrafa sirrikanmu. Sojoji kaɗai za su iya sake daidaita ƙasar nan.”

A wani rubutu daban kuma ya ce: “Dole ne Tinubu ya tafi, kuma dole APC ta mutu kafin Najeriya ta samu daidaito.”

Ana sa ran za a gurfanar da Onukwume, wanda mazaunin Umusayo Layout ne a Karamar Hukumar Oyigbo ta Jihar Ribas a kotu cikin makon nan.

A watan Oktoba, an samu rahotanni da ke nuna cewa wasu jami’an sojoji sun yi yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha

Hukumar EFCC ta tsare tsohon Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami, saboda binciken da ya shafi dawo da wani ɓangare na kuɗaɗen Abacha.

Hukumar ta kira Malami a makon da ya gabata, inda ta yi masa tambayoyi kan wani bincike da ta ke inda ta sake shi daga bisani, amma yanzu ta tsare shi.

Real Madrid  za ta ɓarje gumi da Manchester City a Santiago Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro

Malami ya ce bai aikata komai ba, kuma ba shi da alaƙa da abin da ake zargi.

A cikin wata sanarwa, ya ce: “Ba a taɓa zargina, gayyata ko bincikena game da tallafa wa ta’addanci ba. Duk wani yunƙuri na danganta ni da irin wannan laifi ƙarya ne.”

Ya ƙara da cewa rahotannin kafofin yaɗa labarai ke watsawa sun yi masa mummunar fassara.

“Ba daidai ba ne a ce aikina na gwamnati ya zama hujja ta tallafa wa ta’addanci. A lokacin aikina, na yi aiki tuƙuru wajen ƙarfafa yaƙi da ta’addanci, ba goyon bayansa ba.”

EFCC ba ta fitar da wata sanarwa kan tsare Malami ba.

Haka kuma bai wallafa komai a shafukan sada zumunta ba tsawon kwanaki huɗu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin da miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha