Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
Published: 22nd, November 2025 GMT
Shugaban Cocin Katolika reshen Kontagora, ƙarƙashin ya ce ɗalibai 88 da aka yi zaton sun tsere yayin harin da ’yan ta’adda suka kai a makarantar St Mary Secondary School da ke Papiri, ƙaramar hukumar Agwara ta Jihar Neja, har yanzu ba a san inda suke ba.
A cewar majiyoyi, iyaye da dama sun garzaya makarantar domin kwashe ’ya’yansu bayan harin, amma ba ba su yaran ba.
A baya Aminiya ta ruwaito cewa ’yan bindiga sun kutsa cikin makarantar da daddare a ranar Juma’a, inda suka yi garkuwa da ɗalibai da ma’aikatan makarantar.
Shugaban Cocin Katolika ta Kontagora, Mai Girma Bishop Bulus Dauwa Yohanna, ya sanar ta hannun mai taimaka masa, Daniel Atori, cewa an yi garkuwa da ɗalibai 303, malamai mata huɗu da malamai maza takwas a yayin harin.
Gobara ta lalata gidaje 40 a sansanin ’yan gudun a Borno
Ya ce makarantar na da ɗalibai 430 a ɓangaren firamare, da kuma ɗalibai 199 a ɓangaren sakandare.
Bishop ɗin ya ƙaryata zargin da Sakataran Gwamnatin Jihar Neja ya yi cewa gwamnati ko jami’an tsaro sun yi wa makarantar gargaɗi tun kafin harin.
Ya ce, “Mun tambayi Sakataren Ilimi ko ya samu wata takarda daga gwamnati, ya ce babu; ko an ce ya tura mana wata sanarwa, ma babu. Mun tambaye shi ko an sanar da shi a baki, ya ce a’a. To su faɗa wa duniya wa suka bai wa wannan takarda, ko ta wane hanya aka turo ta?
“Mun kuma tambayar Ƙungiyar Makarantu Masu zaman kansu ta Ƙasa, suma ba su samu wata irin sanarwa ba. Suka ce makarantar an rufe ta kuma an sake buɗe ta kwanaki kaɗan da suka gabata — wannan ma ba gaskiya ba ne. Mu masu bin doka ne,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai Garkuwa Makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Sace ɗalibai: An rufe makarantu a Katsina da Taraba
Gwamnatocin jihohin Katsina da Taraba sun ba da umarnin rufe makarantu sakamakon hare-haren ’yan bindiga da suka sace daruruwan ɗalibai a makarantu a cikin mako guda a jihohin Kebbi da Neja.
Gwamnatin Jihar Taraba ta rufe makarantun kwana a fadin jihar, inda ta ba da umarnin a koma tsarin jeka-ka-dawo sakamakon tabarbarewar tsaro.
Gwamnan Agbu Kefas, ya umarci duk makarantun sakandare na gwamnati da masu zaman kansu da dalibai su daina kwana a makarantu saboda fargabar tsaro a faɗin ƙasar.
Sanarwar da kwamishinar ilimi ta jihar, Augustina Godwin, ya fitar ta ce garkuwa da ɗalibai a Kebbi da Neja ta sanya daliban makarantun kwana zama cikin hadari.
Don haka gwamnati ta umarci komawa tsarin jeka-ka-dawo har sai tsaro ya inganta.
Hakan na zuwa ne a yayin da Gwamnatin Jihar Katsina ta bayar da sanarwar rufe dukkan makarantun gwamnatin, har sai abin da hali yayi.
Sanarwar da ta fito daga Hukumar Ilimin Firamare da Sakandaren jihar a ranar juma’a ta ce, ya ce makarantun za su kasance a rufe har sai an ga ci-gaban da aka samu na yanayin matsalar tsaron da ake fuskanta.
Gwamnatin tace tana nan tana bibiyar yadda sha’anin tsaron yake gudana kafin ɗaukar mataki na gaba.
Waɗannan matakai na zuwa ne bayan ’yan bindiga sun sace ɗalibai kimanin 340 a cikin mako guda a makarantun kwana a jihohin Kebbi da Neja.
A ranar Juma’a aka sace ɗalibai da malamai 315 a makarantar kwana ta St Mary da ke Jihar Neja, kwana huɗu bayan a ranar Litinin sun sace dalibai mata 26 suka kashe jami’an tsaro biyu a makarantar ’yan Mata ta Gwamanti GGCSS da ke yankin Maga a Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu ta Jihar Kebbi.