’Yan ta’adda na kafa doka da karɓar haraji a Arewa — Dambazau
Published: 11th, November 2025 GMT
’Tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida, Laftanar Janar Abdulrahman Bello Dambazau (ritaya), ya bayyana damuwarsa kan yadda matsalar tsaro ta ta’azzara a Arewa, inda ’yan bindiga da ’yan ta’adda suka mamaye wasu yankuna suna kafa dokoki tare da karɓar haraji daga hannun jama’a.
Janar Dambazau ya yi wannan jawabi ne a taron farko na kan tsaro da aka gudanar a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, mai taken “Barazanar Rayuwa da Tsaron Ƙasa.
Ya ce matsalar tsaro a Arewa ba sabuwa ba ce, domin ta wanzu tsawon sama da shekaru 20. “Ana kashe mutane a masallatai a Katsina, Borno, Zamfara da Kano. Arewa ta sha fama da rikicin manoma da makiyaya, ta’addanci da kuma hare-haren ’yan bindiga.
“Mun kai wani matsayi da ’yan ta’adda da ’yan bindiga suka karɓe wasu yankuna, suna karɓar haraji da kuma kafa dokoki a cikinsu.
Sarkin Musulmi ya ba wa makarantu tallafin N1.3bn a Kebbi Matan sojojin da suka mutu na neman agaji“An kashe dubban mutane, an raba miliyoyi da muhallansu. Yawan zawarawa da marayu ya ƙaru, manoma sun rasa gonakinsu, makiyaya kuma sun rasa dabbobinsu — ba tare da wani mataki daga hukumomin gwamnati ba,” in ji shi.
Dambazau ya shawarci gwamnonin Arewa su kafa ma’aikatar ma’adinai a jihohinsu domin haɗa kai da hukumomin tarayya wajen sarrafa albarkatun ƙasa da ke yankunansu, don ƙara samun kuɗaɗen shiga da rage talauci da kuma kawo ƙarshen matsalar tsaro.
Ya kara da cewa, domin magance kashe-kashe da rashin tsaro a Arewa, dole gwamnatocin jihohi su dawo da martabar sarakunan gargajiya, su farfaɗo da harkar noma da yankin ya shahara da ita, su kuma magance matsalar yara marasa zuwa makaranta, tare da tabbatar da haɗa kan jama’a.
“Ina so in jaddada cewa sama da kashi 70 cikin 100 na masu fama da talauci sakamakon rashin tsaro suna Arewa. Tsattsauran ra’ayin addini babban barazana ne ga tsaro a yankin, wanda ya haifar da ƙungiyoyin Boko Haramnda Lakurawa da sauran ’yan ta’adda da ke addabar jama’a,” in ji shi.
Tun da fari, Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya jaddada cewa batun tsaro ya shafi kowa da kowa, yana mai cewa: “Dole mu zauna tare mu tattauna yadda za mu magance wannan matsala.
“A da va haka muke ba. Najeriya ba haka take ba. Idan muka haɗa kai, muka fahimci juna, muka aiwatar da shawarwarin da muka cimma, za mu samu zaman lafiya.”
A nasa ɓangaren, Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, ya ce lokaci ya yi da Arewa za ta haɗe kai domin shawo kan matsalar tsaro da ke addabar ta.
“Ina damuwa da yadda matsalar tsaro ke ƙara kamari a yankin Arewa maso Yamma. Ya kamata wannan taron ya nazarci tushen matsalar — watakila tana da nasaba da sauyin yanayi da wasu abubuwa,” in ji shi.
Shi ma Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya bayyana cewa taron zai bayar da dama wajen tattauna matsalolin da ke addabar Arewa tare da neman mafita mai ɗorewa ga yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan ta adda Arewa hare hare karbar haraji Tsaro matsalar tsaro yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugabar kwamitin wasannin Olympics na duniya (IOC) Kirsty Coventry da kuma shugaban kwamitin na karramawa Thomas Bach a Guangzhou, babban birnin lardin Guangdong da ke kudancin kasar Sin.
Xi ya nuna cewa, kasar Sin ta kasance mai himma, mai ba da kariya kuma mai yayata ruhin wasannin Olympics. Ya ce, gasar wasanni ta kasa ita ce babban bikin wasanni mafi girma a kasar Sin. Kuma yankunan Guangdong, Hong Kong da Macao ne suka hada hannu wajen shirya gasar wasannin ta kasa karo na 15. Ana kyautata zaton cewa, wannan gasar wasannin ta kasa ba wai kawai za ta bayyana sabbin nasarorin da kasar Sin ta samu a sabon zamani ba ne, har ma za ta nuna dimbin abubuwan ci gaba na zamanantarwa mai salo irin na kasar Sin a yankin Guangdong-Hong Kong-Macao.
A nasu bangaren, Kirsty Coventry da Thomas Bach sun bayyana cewa, kwamitin wasannin Olympics na duniya yana godiya ga kasar Sin saboda goyon bayan da take bayarwa na tsawon lokaci, kuma suna fatan ci gaba da karfafa hadin gwiwa da kasar Sin, tare da inganta ci gaban harkokin wasannin Olympics, da kara yada ruhin wasannin na Olympics a duk fadin duniya, da karfafa hadin kai tsakanin al’ummomin dukkan kasashe, da kuma inganta zaman lafiya a duniya.
Kazalika, duk dai a wannan rana, Xi ya gana da wakilan rukunonin gwajin al’amura da na daidaikun mutane a fannin wasanni na kasa da na gasar wasannin motsa jiki, kafin bude gasar wasannin ta kasa ta karo na 15 a Guangzhou. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA