Aminiya:
2025-11-12@15:08:24 GMT

MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa

Published: 12th, November 2025 GMT

Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP), ta ayyana Najeriya ɗaya daga cikin jerin ƙasashen da za su fuskanci matsananciyar yunwa.

Ta kuma yi gargaɗin cewa ƙarin mutane a duniya na iya fuskantar yunwa saboda ƙarancin kuɗin tallafi.

Rahoton da Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) da WFP suka fitar, ya nuna cewa rikice-rikice da tashin hankali ne ke jawo matsananciyar yunwa a ƙasashen da ke cikin hatsari.

DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP

Rahoton ya bayyana ƙasashen Haiti, Mali, Falasdinu, Sudan ta Kudu, Sudan da Yemen a matsayin waɗanda ke cikin mafi munin hali inda jama’a ke fuskantar barazanar yunwa mai tsanani.

Haka kuma, Afghanistan, Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, Myanmar, Najeriya, Somaliya da Siriya sun shiga jerin ƙasashe masu matuƙar damuwa.

Rahoton ya kuma ambaci Burkina Faso, Chadi, Kenya da kuma yanayin ’yan gudun hijirar Rohingya a Bangladesh.

Darakta Janar na WFP, Cindy McCain, ta ce, “Muna fuskantar matsalar yunwa da za a iya kauce mata gaba ɗaya, amma idan ba a ɗauki mataki ba, hakan zai haifar da ƙarin rikici da rashin kwanciyar hankali.”

Rahoton, ya ce kuɗin agajin jin-ƙai yana raguwa sosai, inda aka samu dala biliyan 10.5 kacal daga cikin dala biliyan 29 da ake buƙata don taimaka wa waɗanda ke cikin hatsari.

Saboda ƙarancin kuɗi, WFP ta rage tallafa wa ’yan gudun hijira da waɗanda aka raba da muhallinsu, sannan ta dakatar da shirye-shiryen ciyar da ɗalibai a wasu ƙasashe.

Hukumar FAO kuma ta yi gargaɗin cewa harkar noma na cikin hatsari, wanda shi ne ginshiƙin samar da abinci da hana matsalolin yunwa sake faruwa.

An bayyana cewa tallafi ake buƙata don samar da iri da kula da dabbobi kafin lokacin shuka ko wani sabon rikici ya sake ɓarkewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya Najeriya Ƙasashe yunwa

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yayin da tattaunawa kan makomar ƙungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ke ci gaba da ɗaukar hankali, batun yadda za a haɗa jami’o’i masu zaman kansu cikin tsarin ƙungiyar ya sake tasowa.

Wasu na ganin wannan sabon yunƙuri zai iya zama sabuwar hanyar ƙarfafa hadin kai tsakanin malamai, yayin da wasu ke gargadin cewa hakan na iya kawo tsaiko ga karatun wasu dalibai dake kauracewa jami’oin gwamnati sakamakon yawan yajin aiki da suke tsunduma lokaci zuwa lokaci.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Yaɗuwar Cututtuka A Irin Wannan Lokaci DAGA LARABA: Yadda ‘Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar Makamai

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu
  • Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP
  • Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu
  • An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori
  • ‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU
  • Mazauna Millennium City Sun Zargi Kaduna Electric Da Tilasta Sanya Masu Mita
  • Gwamna Kebbi ya gargaɗi manoma da makiyaya kan su zauna lafiya ko su fuskanci hukunci