Ma’aikatar raya al’adu da yawon bude ido ta kasar Sin ta fitar da sanarwa a jiya Lahadi, wadda ke kira ga al’ummunta da su yi taka-tsantsan a kwanakin nan wajen zuwa yawon bude ido kasar Japan.

Game da hakan, masani a kwalejin bincike ta Nomura Takahide Kiuchi, ya bayyana a jiyan cewa, raguwar yawan Sinawa masu zuwa yawon bude ido Japan, zai haifar da raguwar GDPn kasar ta Japan da kashi 0.

36%, kana hasashen yawan asarar tattalin arziki da hakan zai haifar zai kai JYE tiriliyan 2.2, kwatankwachin kudin Sin yuan biliyan 101.6.

Bayanai sun nuna cewa, kasar Sin ce babbar abokiyar ciniki mafi girma ta Japan, kasa ta biyu mafi girma wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar, kana babban tushen shigar da kayayyaki zuwa kasar. A shekarar 2024, jimillar darajar ciniki tsakanin Sin da Japan ta kai dalar Amurka biliyan 308.3, inda yawan kudin da Sin ta kashe wajen shigo da kayayyaki daga Japan ya kai dalar Amurka biliyan 156.25.

Kididdigar hukuma mai kula da yawon bude ido ta Japan, ta nuna cewa jimillar kudin da masu yawon bude ido na Sin suka kashe a Japan a shekarar 2024 ya haura na al’ummun sauran kasashen duniya.

Manyan ’yan siyasa, da masana masu fashin baki, da kafafen watsa labarai na yankin Taiwan, sun yi Allah wadai da kalaman tayar da husuma na firaministar Japan Sanae Takaichi dangane da yankin Taiwan na Sin, suna masu bayyana kalaman nata a matsayin wadanda suka illata moriyar al’ummun Taiwan, wato mazauna yankin dake fatan wanzuwar zaman lafiya da daidaito a daukacin mashigin Taiwan.

Da yake tsokaci kan hakan, tsohon shugaban jam’iyyar Kuomintang a yankin Taiwan Ma Ying-jeou, ya ce batutuwan da suka shafi bangarori biyu na mashigin Taiwan ba sa bukatar tsoma bakin sassan waje, yana mai jaddada cewa al’ummunsu ne kadai ke da alhakin warware su. Jami’in ya kara da cewa, Sinawa na bangarorin mashigin Taiwan biyu na da basira, da ikon warware sabaninsu cikin lumana.

Shi ma a nasa tsokaci, mawallafin mujallar “Observer” Chi Hsing, cewa ya yi, a yayin mamayar dakarun Japan, al’ummun Taiwan ba su taba dakatar da nuna turjiyarsu ba. Don haka duk wani mai kaunar adalci dake Taiwan zai yi tir da kalaman na firaminista Takaichi.

Hsieh Chih-chuan, mai fashin baki kan batutuwan siyasar Taiwan, ya ce kalaman na Takaichi sun sabawa ainihin tarihi da dokokin kasa da kasa. Daga nan sai ya gargadi ’yan aware masu rajin neman ’yancin kan Taiwan, da kada su yaudari kansu bisa kalaman na Takaichi. Domin kuwa ba makawa Sin za ta kasance kasa daya dunkulalliya.(Saminu Alhassan、Amina Xu)

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95 November 16, 2025 Daga Birnin Sin Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku November 16, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta November 16, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yawon bude ido

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

A gobe Lahadi ne za a wallafa makalar babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, game da ingiza gina sabbin ginshikan samar da ci gaban kasa masu inganci, daidai da yanayin da kasar ta Sin ke ciki.

Za a wallafa makalar ta Xi Jinping, wanda shi ne shugaban kasar Sin, kuma shugaban hukumar zartarwar rundunar sojojin kasar ne a mujallar Qiushi fitowa ta 22 a bana, muhimmiyar mujallar kwamitin kolin JKS. (Saminu Alhassan)

ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo November 15, 2025 Daga Birnin Sin An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka November 15, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan  November 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • Alummar Kasar Ecodo Sun yi Watsi Da Batun Sake Dawo Da Sansanin Sojin Amurka A Kasar
  • Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasa
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
  • Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 
  • Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya