Uwargidan Shugaba Xi Jinping na kasar Sin Peng Liyuan, da Sarauniya Letizia ta kasar Spain, wacce ke rakiyar Sarki Felipe na VI na Spain a ziyarar da ya kawo kasar Sin, sun ziyarci cibiyar gwaji ta kula da nakasassu ta Beijing a yau Laraba.

A cibiyar, Peng da Letizia sun saurari bayanan da aka yi kan ayyukan hidimar nakasassu kuma sun ziyarci wani babban sashen nune-nune na gasar wasannin lokacin hunturu ta nakasassu (Paralympic) ta Beijing da aka yi a shekarar 2022.

Daga nan suka je zauren baje kolin kayayyakin tallafa wa nakasassu da aka kera da manyan fasahohin zamani da kuma sashen karatu na kyauta, inda suka nazarci yadda ake amfani da kayayyakin tallafa wa nakasassu, da ayyukan karatu ga yara nakasassu, da kuma tsarin samar da kayayyakin da ba su da shinge a kasar Sin.

Peng ta ce sha’anin nakasassu yana bukatar hadin gwiwa da goyon baya daga dukkan bangarori domin taimaka musu wajen shiga cikin al’umma.

ADVERTISEMENT

Ta bayyana fatan cewa kasar Sin da Spain za su inganta mu’amala da hadin gwiwa don taimaka wa cimma burin nakasassu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa November 12, 2025 Daga Birnin Sin Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci November 12, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki November 12, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya

Shugaban kasar Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traoré, ya bayyana cewa kasarsa ta zama abin misali a duniya, saboda sauyin da jama’a suka bukata tun lokacin da ya hau mulki a 2022.

“Domin cimma cikakken ‘yancin kai, ya zama dole a bi juyin juya halin inji shi a wani jwabi ta gidan talabijin a jajaribin cika shekaru 65 na samun ‘yancin kai na kasar.

Burkina Faso a yau ta zama misali, abin koyi, kuma tana kan hanya madaidaiciya.

Duniya na kallonmu, kuma ba mu da wani zabi illa mu yi nasara,” in ji Traoré.

A fannin yaki da ta’addanci, shugaban kasar Burkina Faso ya dage cewa sojojin kasar sun kaddamar da hare-hare masu karfi a cikin shekarar da ta gabata a yankunan da a da ake daukar su a matsayin wuraren da abokan gaba ke iko.

An kwace yankuna da dama a cikin wata guda, inda sojojinmu suka kafa sansani.

 “Waɗannan masu laifi waɗanda suka mamaye yankunan ƙasarmu, suna ganin cewa mafakarsu ce, an kore su kuma suna tserewa daga Burkina Faso.

Amma muna gaya musu cewa yanzu suna da zaɓi biyu kawai: su gudu daga Burkina Faso ko su mutu saboda sojojinmu suna kan daga.

Traoré ya yi kira ga mutanen Burkina da su hadu waje daya don tunkarar kalubalen da suka shafi ci gaban kasar, musamman masana’antu da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa don amfanin al’ummar kasar baki ɗaya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannun kan yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu   December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Kamfanin CRCC Ya Kammala Shimfida Hanyar Jirgin Kasa A Gadar Layin Dogo Mafi Tsawo A Afrika Dake Algeria
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya