Aminiya:
2025-11-15@13:41:29 GMT

HOTUNA: Yadda Babban Taronjam’iyyar PDP ke gudana

Published: 15th, November 2025 GMT

.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban taro

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano

Wani babban ɗan Kasuwar Singa da ke Jihar Kano, Alhaji Salisu Abdullahi, ya ce ya yi asarar kaya da kuɗinsu ya haura Naira miliyan 120 a gobarar da ta auku da safiyar ranar Alhamis, wadda ƙone shaguna da yawa.

“An kira ni da misalin ƙarfe 6 na safe, na garzaya zuwa kasuwa, sai kawai na tarar komai ya ƙone.

“Na karɓi kaya bashi a makon da ya gabata domin ci gaba da sayarwa. Yanzu ban san ta yadda zan tunkari masu kayan ba,” in ji shi.

Gobarar, wadda ta fara da misalin ƙarfe 5 na Asuba, ta ƙone shaguna 44 da dukiya mai tarin yawa.

Hukumar Kashe Gobara Jihar Kano, ta ce gobarar ta samo asali ne daga matsalar wutar lantarki a wani gini, wadda daga bisani ta yaɗu zuwa sauran shaguna.

Wani ɗan kasuwa, Musa Abdulhadi, ya ce gobarar ta yaɗu cikin ƙanƙanin lokaci ta yadda ba a samu damar ceto komai ba.

“Gobarar ta yaɗu cikin sauri ƙwarai; ba mu iya fitar da kaya ko ɗaya ba. Na yi asarar kaya na kimanin Naira miliyan takwas.

“Wannan abu ne mai raɗaɗi musamman a wannan mawuyacin hali na tattalin arziƙi da ake ciki,” in ji shi.

Hukumar kashe Gobara ta jihar ta bayyana cewa jinkirin da aka samu wajen kai agaji ya samo asali ne daga manyan motoci da suka toshe hanyoyin shiga kasuwar.

Duk da haka, jami’an hukumar sun samu damar dakatar da gobarar kafin ta bazu zuwa wasu gine-gine.

Wasu ’yan kasuwa sun ɗora laifin tashin gobarar kan amfani da tsohuwar wayar wutar lantarki da rashin kulawa.

Sun ce sun ta yi ƙorafi a baya amma ba a ɗauki mataki ba.

Sun roƙi gwamnati ta tabbatar da ana yin bincike akai-akai a kasuwanni domin kare rayuka da duniyoyin al’umma.

’Yan kasuwar da abin ya shafa sun roƙi Gwamnatin Jihar Kano da masu hannu da shuni da su taimaka musu.

Abdullahi, ya ce: “Muna kira ga gwamnati ta taimaka mana mu sake gina shagunanmu. Da

“Da dama daga cikinmu bashi muka ɗauki kaya domin mu sayar. Idan ba a taimaka mana ba, ba mu san yadda za mu yi ba.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa
  • Mutfwang ya musanta raɗe-raɗin sauya sheƙa zuwa YPP
  • HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya
  • Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki
  • Yadda na yi asarar N120m a gobarar Singa — Ɗan Kasuwar Kano
  • Iraki: Hukumar Zabe Ta Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar
  • Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna