Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Published: 13th, November 2025 GMT
Shugaban jam’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin da shugaban ma’aikatan fadar Shugaban ƙasa, Hon. Femi Gbajabiamila da Dr Abdullahi Umar Ganduje, sun ziyarci zauren Majalisar Wakilai ranar Alhamis domin shaida sauya sheƙar ƴan majalisa biyu daga NNPP zuwa APC.
Ƴan majalisar da suka sauya sheƙar sun haɗa da Hon. Abdulmumin Jibrin, wanda ke wakiltar Kiru/Bebeji a Kano, da Hon. Sagir Koki, wakilin Kano Municipal.
A cikin wasiƙunsu da Kakakin Majalisar Abbas Tajudeen ya karanta, sun bayyana rikici mai sarƙakiya da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar NNPP a matsayin dalilin barin jam’iyyar zuwa APC.
ADVERTISEMENTDuk da jayayya da Hon. Kingsley Chinda daga bangaren marasa rinjaye, wanda ya dage wajen ɗaga batun sanarwar a lokacin karanta wasiƙun da karɓar sauya shekarun, Kakakin Majalisar bai amince da buƙatarsa ba.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAএছাড়াও পড়ুন:
Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi
Adai dai lokacin da ke ta tattaunawa tsakanin Amurka da Indiya kan harkokin kasuwancin , sai ga shi a makon da ya wuce New Delhi ta karbi bakunci daya daga cikin manyan shuwagabannin dake kalubalantar gwamnatin Amurka akan nuna fin karfin a duniya.
Shugaban kasar Rasha viladmir Putin ya kwashe kwanaki biyu a indiya a wata ziyarar aiki da ya kai, kuma wannan yana zuwa ne adaidai lokacin da indiya ke fuskantar harajin da Amurka ta sanya mata na kashi 25 cikin 100 saboda ci gaba da siyan mai a hannun kasar Rasha , lamarin da ya kawo tarnaki a alakar dake tsakanin Delhi da kuma Washinton.
Bugu da kari Amurka ta sanar da takunkumin ne a ranar 23 ga watan oktoba akan manyan kamfanonin mai na kasar Rasha da hakan ha haifar da barazana ga kasar indiya dake neman shigo da man fetur mai sauki daga rasha, sai dai rahotanni sun nuna cewa har yanzu dai kasar indiya itace babbar mai sayan manfetur din kasar Rasha.
Tun a shekara ta 1960 Mosko da New Delhi ke da kyakkayawar dangantaka ta kud da kud da ya hada da kasuwancin , hadin guiwar Soja , kimiyya ,makamashi da kuma sararin samaniya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Iran da Rasha sun jaddada aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa a tsakaninsu December 13, 2025 Ali Nuhu, ya yaba wa Iran kan haskaka Musulinci ta hanyar fina-finai December 13, 2025 MDD ta amince da kudurin da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza December 13, 2025 Benin ta fitar da sammacin kama dan fafutuka Kemi Seba December 13, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan December 12, 2025 Birtaniya Ta yi Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya December 12, 2025 Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci