’Yan bindiga 5 Sun shiga hannun ’yan sanda a Kebbi
Published: 17th, November 2025 GMT
’Yan sanda sun yi nasarar kama wasu ’yan bindiga biyar tare da ƙwace tarin makamai a hannunsu a yankin Zuru–Tadurga da ke Jihar Kebbi.
Rundunar ’yan sanda ta musamman da ta kama su, ta bayyana cewa, ’yan bindiga suna cikin waɗanda suka kai hare-hare a kan al’ummomin Zuru a kwanakin baya.
Ta ƙara da cewa dukkansu ’yan asalin kauyen Birnin Tudu ne da ke cikin ƙananan hukumomin Bukkuyum da Gummi a Jihar Zamfara.
Kakakin ’yan sanda a jihar, CSP Nafiu Abubakar, ya ce makaman da aka ƙwato daga hannun ’yan bindigar sun haɗa bindigogi AK-47 guda 7 a wata ƙaramar gida guda 1 da harbi-ruga guda uku.
’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh GumiSauran sun haɗa da kurtun albarusan AK-47 guda 3 da harsashi 89 da kuma tsabar kuɗi Naira miliyan 2.6
Ya ƙara da cewa an miƙa waɗanda ake zargin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Birnin Kebbi domin ci gaba da bincike da kuma gano sauran abokan aikinsu.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya yaba da jarumta da jajircewar jami’an rundunar tare da ƙarfafa su da kada su yi ƙasa a gwiwa har sai an kawar da matsalar ’yan bindiga da garkuwa da mutane daga jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda hare hare kama yan bindiga yan bindiga Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta gwabza da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo a wasan ƙarshe na tantance wakilin Afrika a share fagen Gasar Cin Kofin Duniya na 2026. Wasan zai ɗauki hankali zai gudana ne a ranar Lahadi a sabon filin Prince Moulay Abdellah da ke Rabat, Morocco, inda za a tantance ƙasa ta ƙarshe daga Afrika da za ta shiga matakin share fagen gasar Kofin Duniya.
Nijeriya ta samu gurbin wasan ƙarshe bayan da ta lallasa Gabon da ci 4-1 a ranar Alhamis, sakamakon da ya ƙarfafa matsayin tawagar wajen sake samun martabarta a nahiyar. A ɗaya ɓangaren, DR Congo ta samu nasarar da ta ba ta gurbin wasan ƙarshe ne bayan da ta doke Kamaru da ci 1-0, inda kyaftin Chancel Mbemba ya zura ƙwallo a mintoci na ƙarshe.
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4A yanzu za a fafata ne tsakanin ƙasashen biyu waɗanda ke neman damar ƙarshe ta wakiltar Afrika a gasar share fagen shiga Kofin Duniya da za a yi a Mexico, Amurka da Kanada. Duk wata gazawa zata ƙare burin kowace tawaga, yayin da nasara za ta buɗe musu ƙofar shiga manyan gasannin duniya.
ADVERTISEMENTWasan na Lahadi zai kasance mai cike da zafi da taka tsantsan, domin dukkan ƙungiyoyin sun shiga Morocco da burin tabbatar da cewa su ne za su samu tagomashi a wasan share fagen, wanda zai zama matakin farko na zuwa babban gasar ta 2026.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA