Jakadan kasar Sin a Japan Wu Jianghao, ya gana da mataimakin ministan harkokin wajen Japan Takehiro Funakoshi a jiya Juma’a, inda ya bayyana matukar adawar kasarsa, da korafi a hukumance, dangane da kalamai marasa dacewa da firaministar Japan Sanea Takaichi ta furta dangane da kasar Sin.

Jakada Wu, ya ce munanan kalamai masu tayar da husuma na Takaichi, dangane da yankin Taiwan na Sin, wadanda aka jiyota tana yi kwanan baya, a majalissar dokokin kasarta sun sabawa hankali, sun tsallaka jan-layin kasar Sin, kana barazanar nuna karfi ne da neman takalar yaki.

Kazalika, firaministar ta Japan ta ki amincewa da kuskurenta, ta ki janye kalaman, ko sassauta mummunan tasirinsu. Don haka matakin nata ya shaida matukar kaucewa gaskiya, da fankamar karfin da ba ta da shi.

Har ila yau, jakada Wu ya ce kalaman na Takaichi sun kasance matukar tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Sin, da keta dokar kasa da kasa, da ka’idojin cudanyar kasashen duniya, da manufar nan ta kasar Sin daya tak a duniya, da keta hurumin takardun siyasa hudu, wadanda Sin da Japan suka daddade, tare da matukar illata odar kasa da kasa bayan yakin duniya na 2, da tushen siyasa na dangantakar Sin da Japan.

ADVERTISEMENT

Daga nan sai jakadan na Sin ya bayyana matukar bacin rai, da kin amincewar kasar Sin da hakan, da kuma mika kakkarfan sakon korafi, da adawa da matsayar firaminista Takaichi. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya November 14, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba November 14, 2025 Daga Birnin Sin Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko November 14, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Da wadannan shaidu na zahiri, muna iya cewa himmar kamfanonin kasar Sin ta fuskar kirkire-kirkiren fasahohi, ya sanya hajojin kasar zama masu tafiya da yanayin zamani, wanda har kullum ake ta kokarin daidaita ci gabansa da bangaren kare muhalli, da aiwatar da matakai na inganta yanayin duniya.

Tun daga yankin kudu maso gabashin Asiya zuwa Turai, daga Latin Amurka zuwa gabas ta tsakiya har Afirka, ana ta ganin karuwar ababen hawa masu aiki da lantarki kirar kasar Sin, a wani yanayin dake shaida kwarewar kamfanonin kasar a fannin kirkire-kirkire fasahohi na zamani, wanda daga karshe ke dacewa da samar da hajoji irin wadanda kasuwannin duniya ke alfahari da kuma bukatar su. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu November 13, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya November 13, 2025 Daga Birnin Sin Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu  November 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta
  • Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
  • Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya
  • Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya
  • Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
  • Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
  • Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci