Leadership News Hausa:
2025-11-15@17:43:46 GMT

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Published: 15th, November 2025 GMT

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

 

Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga Jihar Kano:

Gaskiya ba abu ne mai kyau ba, ka nema ta hanyar halal din ma ya aka kare da kudin yanzu, bale kuma ta hanyar haram. Tsabar son abin duniya ne da rashin tsoron Allah, aji tsoron Allah a nemi halal, a nemi kudi ta tsabtatacciyar hanya.

 

Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, a Jihar Filato:

Wannan maudu’i ne mai matukar muhimmanci, saboda talauci da son zuciya ya yi wa mutane yawa.

Idanun mutane sun rufe, ba sa tunanin ya dace ko bai dace ba. Burinsu kawai shi ne a ina za su samu kudin da za su kashe wutar gabansu, ko kuma su cika burinsu na rayuwa. Lallai kuskure ne babba, a ce mutum ya zama idanunsa sun rufe akan abin duniya, ba ya tsoron Allah akan abin da zai ciyar da iyalinsa. A yayin da mutum ke neman kudi ido rufe, ba ya tunanin lahira ko hakkin wani, ko sakamakon abin da zai same shi, burinsa kawai abin da zai samu. Allah ya sa mu fi karfin zuciyar mu, mu dage da neman halal, mu tsira da mutuncin mu da imanin mu.

 

Sunana Hauwa Abubakar Sarki:

Lokaci ne da Allah ya kaho mu idan ba kana da shi ba ba za a yi da kai ba. Shi ne dalilin da ya sa wasu mutane suka fada neman kudi ta kowani irin hanya. Abun da za a ce shi ne, mu yi hakuri mu zauna a inda Allah ya aje mu, domin kuwa ba kowa ne Allah ya rubuta yana daga cikin masu arziki ba. Talauci shi ne dalili na farko dake janyo hakan da kuma hangen abun hannun wani, ko nace abun da wani ya samu kai ma kace lallai sai ka samu, wanda hakan ba daidai bane. Mu kasance masu taimako kana mu tsaftace neman mu sai mu ga Allah ya albarkaci abun da zamu samu.

 

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri, A Jihar Jigawa:

To magana ta gaskiya rashin yadda da kaddara ce ke jawo haka, domin duk mutumin da ya yadda da kaddara ya san duk wani rabon na dukiya ba zai wuce shi ba don haka ba zai bi hanya mara kyau wajen neman kudi ba. Eh to, dalilan dake jawo hakan suna da yawa, to amma jahilci da rashin tsoron Allah, sune a gaba, domin sune suke jawo haka ga mafi yawan mutane. To hanyoyin dai guda biyu ne, na farko neman ilimin addini domin da shi ne za ka san halak da haramin za kuma ka kiyaye su, sai na biyun tsoron Allah, domin koda kana da ilimi sai kana da tsoron Allah za ka kiyaye halak da haramin.

 

Sunana Hafsat Sa’eed, Jihar Neja:

Taulauci da rashin aikin yi, ga tsadar rayuwa da kullum take karuwa, nauyi na yi wa al’umma yawa suna rasa mafita a rayuwarsu, shi yake haifar da hakan. Wasu kuma son zuciya ne. Kowa ya rika tuna cewa akwai mutuwa, wanda ya yi daidai ya sani, haka ma wanda bai yi ba ya sani.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano, A Jihar Kano:

Neman kudi ya dace, amma ta hanyar halal. Abin da yake kawo hakan talauci da aka jefa al’ummar wannan kasar. Babbar hanyar ita ce, mu ji tsoron Allah muna tuna cewa bawa ba zai taba wuce rabonsa ba. Shawarata a nan ita ce mu tuna cewa babu bawan da zai koma ga ubangijinsa ba tare da ya bar daidai da kwayar zarra na arzikinsa ba, don haka mu tsaya mu nemi halal dinmu domin mu zauna lafiya. Allah ya sa mu dace amin.

 

Sunana Aisha T. Bello, daga Jihar Kaduna:

Gaskiya wasu talauce ne, wasu kuma san abu duniya ne ya yi masu yawa, shi ya sa suke neman kudi ta kowace hanya. Ni na ga wata da idona wanda har sai da nasa baki, amma na ga ta yi nisa ba ta jin kira. Wai za ta kasar waje neman kudi, babu inda ya fi gida dadi. Shawara ta a nan shi ne, in zamu nemi kudi mu neme shi ta hanya mai kyau, kuma mu kula. Allah ya ba mu dace wa.

 

Sunana Abubakar Usman Malam Madori:

A yau, yawaitar matsin rayuwa da kalubalen yau da kullum ya sa mutane da dama ke neman kudi ba tare da la’akari da halal ko haram ba. Wani zai nemi hanyar kirki ya samu na halak, amma wasu kuma za su zabi hanyar da ba ta dace ba kamar sata, damfara, ko karuwanci, duka da nufin biyan bukatunsu na yau da kullum. Wannan hali yana da illa ga dabi’a, addini da tsaron al’umma. Idan kowa zai nemi kudi ta kowacce hanya, to rayuwar al’umma za ta zama barazana, domin ba za a samu gaskiya, aminci da mutunci ba. Mu fahimci cewa arziki na gaskiya yana zuwa ne da hakuri, tawakkali, da bin hanyoyi na gaskiya da halal. Duniya ba za ta kare da wahala ba, amma samun riba ta haram tana da sakamako mai muni a nan duniya da lahira.

 

Sunana Hussy Saniey, daga Katsina:

Rashin tawakkali shi ne linzamin da ke kai wasu mutanen ga aikata haka. Ya kamata a kodayaushe mutane su rika jin tsoron Allah tare da tunawa yana kallonsu a duk wani motsinsu, don haka su kiyaye jikinsu daga haram, domin duk jikin da aka gina da haram ba ya shiga aljanna. Mutane su jajirce a wurin neman halal, duk wanda ya tashi ya nema Allah zai sanya ma shi albarka a cikin neman, a guji cin dukiyar da ba ta da tsarki.

 

Sunana Nura Garba, Tsanyawa, A Jihar Kano:

Yana da alaka da sauyin zamani da al’umma suke son yin kitsan wance amma basu da gashin wance, ga kuma tarun bukatu marasa manufa, da yanzu sai ka ga mutum yana neman kudi ta kowace hanya don kawai ya sai mota irin ta wani. Abin da yake kawo haka shi ne, rayuwar karya da yin gasa da wasu ke yi, sai rashin godiya ta rufin asiri da cikakkiyar lafiyar da Allah ya bawa dan’adam. Hanyoyin magance hakan yadda da samu da rashin na Allah ne, kuma kowa rabonsa zai ci kafin ya bar duniya, don haka ya kamata al’umma su nemi halak ta halastacciyar hanya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Taskira Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko November 8, 2025 Taskira Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu October 19, 2025 Taskira Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi October 12, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Da yake bayanin kan hukumar “Ya ce da akwai rashin bayani dangane da ita hukumar NELFUND, wasu dalibai basu san da akwai ta ba. Akwai kuma wani tunanin da mutane suke yi mi zai sa su tafi makaranta akan bashi?

“Mutane da yawa basu son amsar bashin.Don haka idan mutane basu da yawa, wannan ba kuma yana nufin kamar gwamnatin ta gaza bane, lamarin ya kasance ne domin mutane da yawa basu bukatar neman a basu bashin. Yayin da nake wannan maganar, mai kulawa da harkokin dalibai ya ce akwai dalibai fiye da 3,000 da suke amfana daga shi tsarin na bada bashin kudin makaranta kamar dais hi mataimakin Shugaban Jami’ar ya bayyana,” the BC said.

Da yake bayyana Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Akure , FUTA a matsayin wadda tafiya tare da ita ne a duniya dangane da harkar data shafi ilimi, Farfesa.Oladiji ya ce, makarantar tana tafiya tamkar yadda mutane suke tunanin ko kallonta a matsayin wani wuri ne da ake samun ilimin Boko mai nagarta kamar yadda ya dace,bugu da kari kuma wani wuri ne inda mutum yake daukar mataki na irin yadda yake bukatar cikin ikon Allah ya kasance na dukkan wasu lamurran da suke da alaka da abubuwan da suka shafi karatu gaba daya.

‘’Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya Akure babbar makaranta ce da ta yi suna musamman ma ta bangaren bincike kan lamurran da suka shafi bangaren ilimin fasaha,saboda a samu damar cimmar irin matsalolin da al’umma da duniya suke fuskanta.Hakan abin yake idan aka, tuna da lamarin daya shafi sauyin yanayi da kuma ilimin kimiyyar samaniya,aikin gona, Injiniya, Komfuta da kuma kwarewar lamarrran kafafen sadarwa na zamani.

“A Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya Akure FUTA, mambobi na sassan ita Jami’ar da daibai suna kara kasancewa masu daraja ne da amfani kan lamurran daban- daban a kan lamarin daya shafi karatu ko bada/ koyar da ilimi a duniya, inda suke kasancewa sai an yi tafiya tare da su musamman ma, ta bangaren yin bincike da sanin yadda za a bunkasa abinda aka gano hanyar da za ayi shi. Hakanan ma FUTA bata tsaya ta yi kasa a gwiwa ba domin kuwa tana bada gudunmawa wajen karin haske kan hanyoyin da za abi wajen samar da isasshen abinci a Nijeriya kamar dai yadda Oladiji ya yi nashi karin hasken,”.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ilimi NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu November 8, 2025 Ilimi Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu October 18, 2025 Ilimi Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya
  • Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 
  • Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
  • Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 
  • Nijeriya za ta kece raini da Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
  • Troost-Ekong ya gargaɗi Super Eagles kan wasan da za ta fafata da Gabon
  • Majalisar Dattawa Ta Amince da Karbo Rancen Naira Tiriliyan 1.15 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi