Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
Published: 14th, November 2025 GMT
Kazalika, ta amince da kulla wannan yarjejeniyar ce a shekarar 2023.
A na sa jawabin a wajen kulla yarjejeniyar Babban Shugaban Tashar ta Snake Island Maher Jarmakani ya bayyana wannan hadakar a tsakanin Gwamnatin Tarayya da da Nigerdock mai matukar mahimmanci.
Ya sanar da cewa, yarjejeniyar ta kai ta akalla dala biliyan daya wacce kuma za ta bayar da damar zuba hannun jari daga ketare na kai tsaye, inda hakan zai kuma kara daga matsayin Nijeriya wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci a duniy.
“Mun bi duk matakan da suka kamata domin mu tabatar da cewa, an bi ka’ida bayan amincewa da Tashar ta Snake Island da Gwamnatin Tarayyata yi, “A cewarsa.
Jarmakani ya ci gaba da cewa, wannan jarjejeniyar za ta kara saita Tashar ta Snake Island wanda kuma tare da yin aiki kafada da kafada da Hukumar NPA da Ma’iakatar Kula da Tattalin Arziki na Teku da sauran masu ruwa da tsaki a fannin za samu nasarar kai wa gaci.
“Muna fatan samar da ci gaba a fannin hada-hadar sufurin Jiragen Ruwa tare da kuma samar da sabon ci gaba, da za a amfana daga fannin bunkasa Tattalin Arziki na Teku,” Inji Jarmakani.
A shekarar 2005, Nigerdock, ya bayar da wata damar gudsanar da aiki na shiyya da kuma taimaka wa, wajen kara daga matakin Hukumar NPA, wanda hakan ya sanya, Fadar Shugaban Kasa, ta amince da kafa Tashar ta Snake Island.
Kazalika, NPA da kuma Hukumar Kwastam sun sahalewa Snake Island gudanar da aiki a shekarar 2017.
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: Tashar ta Snake Island Tattalin Arziki
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
Dakarun Sojin Rundunar Operation Haɗin Kai, sun kashe ’yan ta’adda biyu a wani samame da suka kai yankin Shettimari da ke Ƙaramar Hukumar Konduga, a Jihar Borno.
Majiyoyi sun shaida cewa rundunar ta kai harin ne ƙarƙashin Operation Desert Sanity V da safiyar ranar Alhamis.
Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a BinuwaiWata majiyar soji ta ce, “Sojojin sun tare mayaƙan a kusa da inda suka ke shirin kai hari a yankin da misalin ƙarfe 1:20 na dare.”
Ya ƙara da cewa, “Sojojin sun yi nasarar daƙile ’yan ta’addan nan take, inda suka kashe biyu daga cikinsu yayin da wasu suka tsere.”
Bugu da ƙari, majiyar ta ce daga baya an gano wasu bama-bamai guda biyu da kuma wani gidan harsashi guda ɗaya mai ɗauke da harsasai 23 masu ɗangon 7.62mm x 39mm da ’yan ta’addan suka watsar yayin tserewa.
Majiyar ta ƙara da cewa, “Babu wanda ya mutu a cikin sojojin, sai dai daga baya tawagar sojojin sun ci gaba da aikinsu.”