Leadership News Hausa:
2025-11-16@08:26:58 GMT

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Published: 16th, November 2025 GMT

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

 

Ɓangaren Shari’a a Nijeriya, yana da alhakin bayyana dokoki, kare kundin tsarin mulki, da kuma tabbatar da adalci. An tsara tsarin shari’a a karkashin jagorancin Kotun Ƙoli inda Alƙalin Alƙalan Nijeriya (CJN) ke kula da ita, sannan Kotun Ɗaukaka Ƙara da Manyan Kotuna a matakin jiha da tarayya.

 

Daga cikin manyan haƙƙoƙin da suka rataya akan ɓangaren Shari’a, akwai fassara kundin tsarin mulki da dokoki don amfani da su a shari’o’i.

Sulhunta masu saɓani da kare haƙƙin ‘yan ƙasa da kuma tabbatar da cewa, sauran sassan gwamnati suna aiki a cikin iyakokin kundin tsarin mulki.

 

Amma, mu tambayi kanmu, wai me ke faruwa a ɓangaren Shari’a, ake samun hukuncin Shari’a ɗaya masu karo da juna?

 

An samu ruɗani a Kano a ranar Talata, 29 ga Mayu, 2024 bayan wani umarnin kotu guda biyu masu karo da juna game da taƙaddamar da ta taso kan sarautar Masarautar Kano tsakanin Sarki Muhammadu Sanusi na II da Aminu Ado Bayero, sarkin da aka sauke.

 

Yayin da Mai Shari’a S. Amobeda na Babbar Kotun Tarayya, Kano, ya umarci Sufeto Janar na ‘Yansanda, Kayode Egbetokun, da Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kano, Hussain Gumel, da su tabbatar da cewa, an bai wa Aminu Ado Bayero dukkan haƙƙoƙin gata da ake bai wa sarakuna, nan take kuma, Mai Shari’a Amina Aliyu ta Babbar Kotun Jihar Kano ta hana ‘yansanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da Sojojin Nijeriya korar Muhammadu Sanusi na II, Sarkin Kano da aka dawo da shi kan kujerar sarautar.

 

Taƙaddamar dai ta fara ne a lokacin da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauke Bayero daga kan sarautar Masarautar Kano, tare da wasu Sarakuna huɗu na Rano, Bichi, Karaye da Gaya inda kuma ya mayar da Lamido Sanusi a matsayin Sarki bayan soke dokar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya yi amfani da ita wajen sauke shi daga kujerar mulki a shekarar 2020.

 

Da yake magana kan halin da ake ciki a Kano, wani lauya mazaunin Abuja, Kennedy Khanoba, yayin da yake tattaunawa da Jaridar PUNCH ya roƙi Shugaba Bola Tinubu da ya bar doka ta yi aiki, a ajiye maganar siyasa a gefe, yanzu doka tana hannun gwamnan jihar.

 

Har ila yau, Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta nuna rashin jin daɗi game da hukunce-hukuncen da ke karo da juna daga kotuna.

 

Ƙungiyar lauyoyin ta yi wannan kira ne yayin da take yi wa ‘yan jarida bayani kafin Makon Shari’a na 2025, inda ta kuma yi kira da a yi gyare-gyare don daidaita shari’o’in kafin zaɓen dake tafe a ƙasar.

 

Sai dai, shugaban na NBA reshen Akure, ya yi karin haske da cewa, “wani lokacin, yanke hukuncin masu karo da juna, suna tasowa ne daga bambance-bambancen ra’ayoyin alkalai” kuma ya amince cewa Majalisar Shari’a ta Ƙasa (NJC) tana ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yanayi. Yayin da wasu masu ruwa da tsaki a ɓangaren Shari’a ke zargin ke zargin ɓangaren zartarwa da tsoma baki a Shari’o’in da suke da wani ra’ayi na musamman akai.

 

To, ko meye ke haifar da wannan hukunce-hukuncen masu bugu da juna?

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Da ɗumi-ɗuminsa Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7 November 15, 2025 Manyan Labarai Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso November 15, 2025 Manyan Labarai NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama November 15, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Ta ce, “Kungiyar ta fi kai hare-hare a shagunan EE, inda suke amfani da barazana da tashin hankali wajen tilasta ma’aikata su bude dakunan ajiya na sirri kafin su gudu da wayoyi masu tsada da sauran na’urori.”

A jimlace, sun sace kayayyaki da darajarsu ta kai fam miliyan £240,000.

Jami’an tsaro sun gano masu laifin ta hanyar shaidar DNA, da kuma bayanan kira da rikodin motocin da suka yi amfani da su.

An ce sun ci gaba da bibiyar kungiyar yayin da take shirin sake kai wani hari, inda a ranar 19 ga Nuwamba, 2024, jami’ai suka yi musu kwanton bauna suka kama mutane hudu daga cikinsu a lokacin da suke kokarin yin fashi a wani shagon EE da ke Kilburn.

“Bincike a gidajen da ake danganta su da wadanda ake zargin ya kai ga gano kayan da aka sace da karin shaidu da ke hada kungiyar da fashi-fashin.”

Sanarwar ta bayyana cewa mutane 10 da aka kama a lokacin aikin an gurfanar da su a kotu, inda takwas suka amsa laifi na hadin gwiwa wajen fashi a ranar 30 ga Janairu.

Sanarwar ta kara da cewa bayan amsa laifin, an yanke musu hukuncin a ranar Jumma’a, 7 ga Nuwamba.

Ta bayyana tsawon lokacin da za su yi a gidan yari kamar haka:

James Adodo na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 10 a gidan yari.

Dabid Akintola na Samuel Street, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 6 a gidan yari.

Michael Babo na Gilbert Close, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 10 a gidan yari.

Robert Hills na Mayfield Road, Grabesend, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 5 da watanni 3 a gidan yari.

Ayomide Olaribiro na Warrior Skuare, Manor Park, an yanke masa hukuncin shekaru 4 da watanni 6 a gidan yari.

Nelson Joel na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 3 a gidan yari.

Olabiyi Obasa na Norfolk Close, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 6 a gidan yari.

Dabid Okewole na Bale Road, Northfleet, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 7 da watanni 6 a gidan yari.

Sanarwar ta kuma nuna cewa wasu da aka yi kara biyu sun amsa laifin kokarin fashi, inda aka yanke musu hukuncin da ya dace.

Labille Bloise na Goldcrest Close, Thamesmead, an yanke masa hukuncin shekaru 2, wanda aka dage har tsawon shekaru 2.

Mushtakim Miah na Artillery Place, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 8 da watanni 6 a gidan yari.

Wannan shari’a ta zo ne a daidai lokacin da ake karuwa da rahotannin ’yan Nijeriya da ke kasashen waje da ake yanke musu hukuncin laifuka.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a ranar Laraba da ta gabata cewa wani dalibi dan Nijeriya mai digiri na biyu da ke zaune a Birtaniya, Chiemka Okoronta, zai yi kaura daga kasar bayan ya yi zaman gidan yari na shekaru 10, saboda an same shi da laifin fyade kan wata yarinya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Kotu Da Ɗansanda ’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi November 15, 2025 Kotu Da Ɗansanda NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano November 14, 2025 Kotu Da Ɗansanda An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
  • Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo
  • Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
  • Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
  • Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
  • Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan
  • Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
  • Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu