PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu
Published: 15th, November 2025 GMT
Jam’iyyar PDP ta kori Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da tsohon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Samuel Anyanwu.
PDP ta yanke wannan hukunci ne a babban taron jam’iyyar da ake gudanarwa a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.
Gwamnati, UNICEF da ’yan jarida sun haɗa don yaƙar cututtukan da aka manta da su a Gombe Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — KwankwasoTsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na yankin Kudu, Cif Olabode George ne, ya gabatar da ƙudirin korarsu, sannan Samaila Burga, shugaban PDP na Jihar Bauchi, ya mara masa baya.
A baya, tsagin jam’iyyar da ke goyon bayan Wike sun kai ƙara kotu don a hana gudanar da taron.
Amma PDP ta samu hukuncin da ya ba ta damar ci gaba da taron daga Kotun Ƙoli ta Jihar Oyo.
Kwana biyu kafin taron, Mao Ohuabunwa, Shugaban Majalisar Amintattu (BoT) na ɓangaren Wike, ya ce duk wanda ya tafi Ibadan don taron hutu ya je yi, domin doka ba za ta aminta da shi ba.
A cewarsa, Anyanwu ya riga ya fitar da sanarwar ɗage taron.
Ohuabunwa ya ce: “Mun zauna a matsayin kwamitin zartarwa na ƙasa na PDP, muka duba abubuwan da muka yi. Mun yadda da bin hukuncin kotu game da taron Ibadan. Don haka ba mu da hannu a taron.
“Ibadan wurin jama’a ne, mutane na iya zuwa don kowane abu amma ba don babban taro ba. Duk wanda ya tafi can da sunan taro ya ɗauki hakan a matsayin shaƙatawa kawai.
“Ba za mu amince da take haƙƙin kundin tsarin mulki da wasu mutanen ke yi da sunan babban taro ba.”
Muƙaddashin shugaban tsagin, Abdulrahman Muhammad, shi ma ya kira wakilansu da su guji zuwa taron.
Ya ce tsagin nasu zai ci gaba da haɗa kan mambobi a jihohi 36 da Abuja domin ƙarfafa jam’iyyar.
Muhammad ya ce: “Muna kiran dukkanin wakilai su guji zuwa taron Ibadan.”
A nasa jawabin, Wike ya gode wa mambobin jam’iyyar saboda yadda suke tsayawa wajen kare jam’iyyar a yankunansu.
Ya ce su a ɓangarensu za su ci gaba da bin doka kuma ba za su bari a tsoratar da su ba.
Wike, ya kuma ce ba zai taɓa yaudarar waɗanda ke goyon bayan kundin tsarin mulkin jam’iyyar ba.
Ya ce: “Ina farin ciki da yadda kuke nuna damuwa game da jam’iyyar a yankunanku. Zan ci gaba da goyon bayanku, ba zan yaudare ku ba.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
Babban taron dandalin kafafen yada labarai na kasashe masu tasowa da kwararru na kawancen Sin da Afirka da aka bude a jiya Alhamis a birnin Johannesburg da ke kasar Afirka ta Kudu, zai lalubo hanyoyin karfafa hadin gwiwa, da fadada yin magana da murya daya a tsakanin kasashe masu tasowa da kuma habaka gudanar da tsarin shugabancin duniya na bai-daya.
Wanda kamfanin dillancin labarai na Xinhua, da Tarayyar Afirka (AU) da kamfanin Independent Media na kasar Afirka ta Kudu da sauran abokan hulda suka shirya, taron na kwanaki biyu ya samu halartar wakilai sama da 200 daga kafofin watsa labarai fiye da 160, da kungiyoyin kwararru, da hukumomin gwamnati da sauran cibiyoyi daga kasar Sin da kasashen Afirka 41, da kuma kungiyar AU.
A karkashin taken “garambawul ga tsarin shugabancin duniya: sabbin rawar da za a taka da kudurori na hangen nesa ga hadin gwiwar Sin da Afirka,” taron ya mayar da hankali ne kan yadda hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labarai da kungiyoyin kwararru zai iya ba da gudummawa wajen tsara shugabanci na duniya mafi adalci da ya hade kowa da kowa.
ADVERTISEMENTTaron ya kuma kunshi fitar da wani rahoto na kwararru mai taken “gina sabon tsarin shugabancin duniya–yin aiki tare don neman samar da tsarin shugabancin duniya mai adalci da ma’ana,” da kuma kaddamar da turbar sadarwa ta hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa mai lakabin “hadin kai a cikin zukata, hanya da kuma aiki–shirin aiki kan karfafa hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2026.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA