Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba
Published: 16th, November 2025 GMT
Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya ce zai fice daga jam’iyyar PDP tare da sauya sheƙa zuwa APC a hukumance a ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamba.
Ya bayyana haka ne yayin da yake duba aikin gyaran Filin Wasanni na Jolly Nyame da ke Jalingo a ƙarshen mako.
Ba da yawuna PDP ta kori Wike ba — Muftwang Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasaYayin da yake magana da ’yan jarida, Gwamna Kefas, ya ce ya yanke shawarar ficewa daga PDP ne saboda nemo hanyar da zai amfanar da al’ummar Taraba.
Ya ce: “Zan sauya sheƙa a hukumance daga PDP zuwa APC a ranar 19 ga watan Nuwamba. Wannan sauyi zai amfanar da al’ummar Taraba.”
Ya ƙara da cewa ana ci gaba da shirye-shiyen bikin tarbarsa.
Da aka tambaye shi ko akwai wani sharaɗi da aka gindaya masa kafin ya sauya sheƙa, ya ce babu ko ɗaya.
Mambobin Majalisar Zartarwa ta jihar sun nuna cikakken goyon bayansu ga gwamnan.
Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, Muslim Aruwa, wanda ya yi magana a madadin sauran kwamishinoni, ya ce dukkanin muƙarraban gwamnan za su bi shi zuwa APC.
Ya ce: “Gwamna shi ne shugabanmu, duk inda ya je muna tare da shi.”
Aruwa, ya bayyana cewa shiga jam’iyyar da mulkin tarayya zai samar wa jihar ci gaba.
Ya ƙara da cewa: “Wannan sauya sheƙa na mutanen Taraba ne baki ɗaya, kuma muna tare da shi ɗari bisa ɗari.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sauya Sheƙa Taraba sauya sheƙa
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu
Yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Comoros Azali Assoumani, sun aika wa juna sakon taya murnar cika shekaru 50 da kulla alakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu.
A cikin sakonsa, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, yana mayar da hankali sosai kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Comoros, kuma yana son hada hannu da shugaba Azali, da amfani da cikar alakar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu shekaru 50, a matsayin wata dama ta ciyar da dangantakarsu ta gargajiya gaba, da ma inganta tabbatar da nasarorin da aka cimma a yayin taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC), da bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Comoros bisa manyan tsare-tsare, da kuma kara taka rawar gani wajen gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta Sin da Afirka ta ko wane lokaci a sabon zamani.
A nasa bangaren, shugaba Azali ya bayyana cewa, bisa yanayin da duniya ke ciki na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice, ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya gabatar na girmama ikon mulkin kai da rashin tsoma baki cikin harkokin gidan kasa da kasa tare kuma da cimma nasara tare ta hanyar hadin kai, ya kara wa kasashe masu tasowa kwarin gwiwa, ciki har da kasar Comoros. Ya ce kasarsa na son yin kokari tare da kasar Sin bisa ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adam, don karfafa samun dauwamamman ci gaba irin na hakuri da juna, da ba da gudummawa ga inganta hadin kai da ma samun wadata tare a tsakanin Afirka da Sin. (Bilkisu Xin)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA