Aminiya:
2025-11-17@07:26:10 GMT

NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar

Published: 17th, November 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Matsayar doka ta zama babbar abun tattaunawa a Najeriya yayin da jam’iyyar PDP ta gudanar da taron ta na kasa duk da mabanbantan hukunce hukunce daga kotuna biyu.

 

Umarnin kotu guda yana goyon bayan taron, ɗayan kuwa ya haramta shi gaba ɗaya. Wadannan hukunce hukunce ba baiwa jam’iyyar damar yi ko haramta musu taron kadai suka yi ba, harda baiwa hukumar zabe ta kasa umurnin saka ido ko haramta musu wannan dama yayin taron.

Duk da wadannan hukunce hukunce, jam’iyyar ta gudanar da taron inda ta zabi shugabannin da zasu cigaba da jan ragamar al’amuranta da kuma daukar wasu kwararan matakai.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jam iyyar PDP

এছাড়াও পড়ুন:

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

 

Ɓangaren Shari’a a Nijeriya, yana da alhakin bayyana dokoki, kare kundin tsarin mulki, da kuma tabbatar da adalci. An tsara tsarin shari’a a karkashin jagorancin Kotun Ƙoli inda Alƙalin Alƙalan Nijeriya (CJN) ke kula da ita, sannan Kotun Ɗaukaka Ƙara da Manyan Kotuna a matakin jiha da tarayya.

 

Daga cikin manyan haƙƙoƙin da suka rataya akan ɓangaren Shari’a, akwai fassara kundin tsarin mulki da dokoki don amfani da su a shari’o’i. Sulhunta masu saɓani da kare haƙƙin ‘yan ƙasa da kuma tabbatar da cewa, sauran sassan gwamnati suna aiki a cikin iyakokin kundin tsarin mulki.

 

Amma, mu tambayi kanmu, wai me ke faruwa a ɓangaren Shari’a, ake samun hukuncin Shari’a ɗaya masu karo da juna?

 

An samu ruɗani a Kano a ranar Talata, 29 ga Mayu, 2024 bayan wani umarnin kotu guda biyu masu karo da juna game da taƙaddamar da ta taso kan sarautar Masarautar Kano tsakanin Sarki Muhammadu Sanusi na II da Aminu Ado Bayero, sarkin da aka sauke.

 

Yayin da Mai Shari’a S. Amobeda na Babbar Kotun Tarayya, Kano, ya umarci Sufeto Janar na ‘Yansanda, Kayode Egbetokun, da Kwamishinan ‘Yansanda na Jihar Kano, Hussain Gumel, da su tabbatar da cewa, an bai wa Aminu Ado Bayero dukkan haƙƙoƙin gata da ake bai wa sarakuna, nan take kuma, Mai Shari’a Amina Aliyu ta Babbar Kotun Jihar Kano ta hana ‘yansanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da Sojojin Nijeriya korar Muhammadu Sanusi na II, Sarkin Kano da aka dawo da shi kan kujerar sarautar.

 

Taƙaddamar dai ta fara ne a lokacin da gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauke Bayero daga kan sarautar Masarautar Kano, tare da wasu Sarakuna huɗu na Rano, Bichi, Karaye da Gaya inda kuma ya mayar da Lamido Sanusi a matsayin Sarki bayan soke dokar da tsohon gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya yi amfani da ita wajen sauke shi daga kujerar mulki a shekarar 2020.

 

Da yake magana kan halin da ake ciki a Kano, wani lauya mazaunin Abuja, Kennedy Khanoba, yayin da yake tattaunawa da Jaridar PUNCH ya roƙi Shugaba Bola Tinubu da ya bar doka ta yi aiki, a ajiye maganar siyasa a gefe, yanzu doka tana hannun gwamnan jihar.

 

Har ila yau, Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya (NBA) ta nuna rashin jin daɗi game da hukunce-hukuncen da ke karo da juna daga kotuna.

 

Ƙungiyar lauyoyin ta yi wannan kira ne yayin da take yi wa ‘yan jarida bayani kafin Makon Shari’a na 2025, inda ta kuma yi kira da a yi gyare-gyare don daidaita shari’o’in kafin zaɓen dake tafe a ƙasar.

 

Sai dai, shugaban na NBA reshen Akure, ya yi karin haske da cewa, “wani lokacin, yanke hukuncin masu karo da juna, suna tasowa ne daga bambance-bambancen ra’ayoyin alkalai” kuma ya amince cewa Majalisar Shari’a ta Ƙasa (NJC) tana ƙoƙarin kawo ƙarshen wannan yanayi. Yayin da wasu masu ruwa da tsaki a ɓangaren Shari’a ke zargin ke zargin ɓangaren zartarwa da tsoma baki a Shari’o’in da suke da wani ra’ayi na musamman akai.

 

To, ko meye ke haifar da wannan hukunce-hukuncen masu bugu da juna?

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Da ɗumi-ɗuminsa Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7 November 15, 2025 Manyan Labarai Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso November 15, 2025 Manyan Labarai NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama November 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
  • An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing
  • Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu
  • NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
  • Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar
  • Kotu ta sake hana PDP gudanar da babban taronta na ƙasa