Aminiya:
2025-11-14@06:53:29 GMT

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman Rani

Published: 14th, November 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A duk shekara bayan girbin damina, ana sa ran manoma su ci gaba da noma a lokacin rani domin tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arziki. Sai dai hakan na fuskantar kalubale da dama da ke hana yawancin manoma shiga noman rani.

 

Kamar yadda masana suka sha bayyanawa, akwai dalilai da dama dake hana manoma shiga noman rani a duk lokacin da aka ce damina ta tattara inata intat.

Shin ko wadanne kalubale ne ke hana manoma shiga noman rani bayan damuna ta wuce?

NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya DAGA LARABA: Tasirin Da Tura Jami’an ‘Yan Sanda Kare Manyan Mutane Zai Haifar Ga Tsaron Al’umma

Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Noman rani

এছাড়াও পড়ুন:

MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa

Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP), ta ayyana Najeriya ɗaya daga cikin jerin ƙasashen da za su fuskanci matsananciyar yunwa.

Ta kuma yi gargaɗin cewa ƙarin mutane a duniya na iya fuskantar yunwa saboda ƙarancin kuɗin tallafi.

Rahoton da Hukumar Abinci da Noma ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) da WFP suka fitar, ya nuna cewa rikice-rikice da tashin hankali ne ke jawo matsananciyar yunwa a ƙasashen da ke cikin hatsari.

DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu Ɗan Majalisar Wakilai daga Kano Sagir Ƙoƙi ya fice daga NNPP

Rahoton ya bayyana ƙasashen Haiti, Mali, Falasdinu, Sudan ta Kudu, Sudan da Yemen a matsayin waɗanda ke cikin mafi munin hali inda jama’a ke fuskantar barazanar yunwa mai tsanani.

Haka kuma, Afghanistan, Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, Myanmar, Najeriya, Somaliya da Siriya sun shiga jerin ƙasashe masu matuƙar damuwa.

Rahoton ya kuma ambaci Burkina Faso, Chadi, Kenya da kuma yanayin ’yan gudun hijirar Rohingya a Bangladesh.

Darakta Janar na WFP, Cindy McCain, ta ce, “Muna fuskantar matsalar yunwa da za a iya kauce mata gaba ɗaya, amma idan ba a ɗauki mataki ba, hakan zai haifar da ƙarin rikici da rashin kwanciyar hankali.”

Rahoton, ya ce kuɗin agajin jin-ƙai yana raguwa sosai, inda aka samu dala biliyan 10.5 kacal daga cikin dala biliyan 29 da ake buƙata don taimaka wa waɗanda ke cikin hatsari.

Saboda ƙarancin kuɗi, WFP ta rage tallafa wa ’yan gudun hijira da waɗanda aka raba da muhallinsu, sannan ta dakatar da shirye-shiryen ciyar da ɗalibai a wasu ƙasashe.

Hukumar FAO kuma ta yi gargaɗin cewa harkar noma na cikin hatsari, wanda shi ne ginshiƙin samar da abinci da hana matsalolin yunwa sake faruwa.

An bayyana cewa tallafi ake buƙata don samar da iri da kula da dabbobi kafin lokacin shuka ko wani sabon rikici ya sake ɓarkewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji A Najeriya
  • Super Falconets ta lashe gasar WAFU ta ’yan ƙasa da shekaru 20
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza
  • Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu
  • Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Malaman Jami’oi Masu Zaman Kansu Na Shiga Kungiyar ASUU