Leadership News Hausa:
2025-11-15@12:33:29 GMT

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Published: 15th, November 2025 GMT

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Da yake bayanin kan hukumar “Ya ce da akwai rashin bayani dangane da ita hukumar NELFUND, wasu dalibai basu san da akwai ta ba. Akwai kuma wani tunanin da mutane suke yi mi zai sa su tafi makaranta akan bashi?

“Mutane da yawa basu son amsar bashin.Don haka idan mutane basu da yawa, wannan ba kuma yana nufin kamar gwamnatin ta gaza bane, lamarin ya kasance ne domin mutane da yawa basu bukatar neman a basu bashin.

Yayin da nake wannan maganar, mai kulawa da harkokin dalibai ya ce akwai dalibai fiye da 3,000 da suke amfana daga shi tsarin na bada bashin kudin makaranta kamar dais hi mataimakin Shugaban Jami’ar ya bayyana,” the BC said.

Da yake bayyana Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya dake Akure , FUTA a matsayin wadda tafiya tare da ita ne a duniya dangane da harkar data shafi ilimi, Farfesa.Oladiji ya ce, makarantar tana tafiya tamkar yadda mutane suke tunanin ko kallonta a matsayin wani wuri ne da ake samun ilimin Boko mai nagarta kamar yadda ya dace,bugu da kari kuma wani wuri ne inda mutum yake daukar mataki na irin yadda yake bukatar cikin ikon Allah ya kasance na dukkan wasu lamurran da suke da alaka da abubuwan da suka shafi karatu gaba daya.

‘’Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya Akure babbar makaranta ce da ta yi suna musamman ma ta bangaren bincike kan lamurran da suka shafi bangaren ilimin fasaha,saboda a samu damar cimmar irin matsalolin da al’umma da duniya suke fuskanta.Hakan abin yake idan aka, tuna da lamarin daya shafi sauyin yanayi da kuma ilimin kimiyyar samaniya,aikin gona, Injiniya, Komfuta da kuma kwarewar lamarrran kafafen sadarwa na zamani.

“A Jami’ar fasaha ta gwamnatin tarayya Akure FUTA, mambobi na sassan ita Jami’ar da daibai suna kara kasancewa masu daraja ne da amfani kan lamurran daban- daban a kan lamarin daya shafi karatu ko bada/ koyar da ilimi a duniya, inda suke kasancewa sai an yi tafiya tare da su musamman ma, ta bangaren yin bincike da sanin yadda za a bunkasa abinda aka gano hanyar da za ayi shi. Hakanan ma FUTA bata tsaya ta yi kasa a gwiwa ba domin kuwa tana bada gudunmawa wajen karin haske kan hanyoyin da za abi wajen samar da isasshen abinci a Nijeriya kamar dai yadda Oladiji ya yi nashi karin hasken,”.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ilimi NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu November 8, 2025 Ilimi Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu October 18, 2025 Ilimi Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma October 18, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnatin ta

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban taron dandalin kafafen yada labarai na kasashe masu tasowa da kwararru na kawancen Sin da Afirka da aka bude a jiya Alhamis a birnin Johannesburg da ke kasar Afirka ta Kudu, zai lalubo hanyoyin karfafa hadin gwiwa, da fadada yin magana da murya daya a tsakanin kasashe masu tasowa da kuma habaka gudanar da tsarin shugabancin duniya na bai-daya.

Wanda kamfanin dillancin labarai na Xinhua, da Tarayyar Afirka (AU) da kamfanin Independent Media na kasar Afirka ta Kudu da sauran abokan hulda suka shirya, taron na kwanaki biyu ya samu halartar wakilai sama da 200 daga kafofin watsa labarai fiye da 160, da kungiyoyin kwararru, da hukumomin gwamnati da sauran cibiyoyi daga kasar Sin da kasashen Afirka 41, da kuma kungiyar AU.

A karkashin taken “garambawul ga tsarin shugabancin duniya: sabbin rawar da za a taka da kudurori na hangen nesa ga hadin gwiwar Sin da Afirka,” taron ya mayar da hankali ne kan yadda hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labarai da kungiyoyin kwararru zai iya ba da gudummawa wajen tsara shugabanci na duniya mafi adalci da ya hade kowa da kowa.

ADVERTISEMENT

Taron ya kuma kunshi fitar da wani rahoto na kwararru mai taken “gina sabon tsarin shugabancin duniya–yin aiki tare don neman samar da tsarin shugabancin duniya mai adalci da ma’ana,” da kuma kaddamar da turbar sadarwa ta hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa mai lakabin “hadin kai a cikin zukata, hanya da kuma aiki–shirin aiki kan karfafa hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2026.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta November 14, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G November 14, 2025 Daga Birnin Sin Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne November 14, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
  • Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
  • Mutum ɗaya ya rasu yayin da ’yan sanda da ’yan bindiga suka yi artabu a Kwara
  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe
  • Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
  • Jihar Jigawa Za ta Kashe Sama da Naira Biliyan Daya Domin Inganta Ayyukan Wutar Lantarki