Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
Published: 16th, November 2025 GMT
Kalaman tayar da husuma na firaministar Japan Sanae Takaichi, dangane da batun yankin Taiwan na kasar Sin, na ci gaba da shan suka da Allah wadai daga sassan kasa da kasa. Wani sakamakon kuri’un jin ra’ayin al’umma da kafar CGTN ta gabatar ya nuna yadda akasarin masu bayyana mahanga suka amince da cewa, matakin na Takaichi tsoma baki ne cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma akwai bukatar gaggauta sanya ido kan karuwar burikan wasu jagororin Japan masu tsattsauran ra’ayi, na ruguza odar kasa da kasa ta bayan yakin duniya na biyu.
Kaso 91.1 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin na ganin kamata ya yi Japan ta gyara tarihin ta’asar da ta aikata ta hanyar aiwatar da matakai na hakika, ta kuma martaba dukkanin ikon mulkin kai da kare kimar yankunan kasar Sin. Kazalika, kaso 88.5 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin sun soki lamirin yadda Japan ta yi karan-tsaye ga odar kasa da kasa ta bayan yakin duniya na biyu.
Bugu da kari, kaso 86.1 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin sun soki kalaman Takaichi, ganin yadda suka yi matukar keta tanade-tanade na hakika, dangane da batun yankin na Taiwan, da keta hurumin takardun siyasa hudu wadanda Sin da Japan suka daddade, wanda hakan ya yi matukar illata tushen alakar Sin da Japan.
ADVERTISEMENTHar wa yau, kaso 88.9 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin sun yi Allah wadai da kalaman Japan, na yunkurin tsoma baki cikin batun Taiwan, da yi wa kasar Sin barazanar soji, suna masu cewa irin wadannan kalamai za su yi matukar barazana ga zaman lafiya da daidaito a shiyyar. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKAকীওয়ার্ড: bisa dari na masu bayyana ra ayoyin
এছাড়াও পড়ুন:
Yahudawa sun banka wa masallaci wuta a Yammacin Kogin Jodan
Wasu Yahudawa ’yan kama-wuri-zauna sun lalata tare da kona wani masallaci da ke gabar yammacin kogin Jodan da Isra’ila ta mamaye, kamar yadda kamfanin dillancin Labarai na Falasɗinu (WAFA) ya ruwaito a ranar Alhamis.
WAFA ya ce Yahudawan sun kuma yi rubuce-rubucen batanci a bangon masallacin da ke cikin wani ƙauye a arewa maso yammacin yankin, da safiyar ranar.
HOTUNA: NDLEA ta ƙone tan dubu 52 na miyagun ƙwayoyi a Zariya NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Manoman Najeriya Noman RaniWasu kafafen yaɗa labarai kuma sun ce rubuce-rubucen da aka fesa da fenti sun haɗa da cin mutuncin Annabi Muhammad (SAW) da harshen Ibrananci.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana gudanar da bincike kan zargin.
Babu rahoton rauni ko mutuwa a lamarin kawo yanzu, amma bidiyon da ke yawo a kafafen yada labaran Falasɗinu da Isra’ila sun nuna lalacewar masallacin.
Shugaban Isra’ila, Isaac Herzog, ya bayyana harin a matsayin “mai matuƙar daure kai.”
Herzog ya ce wannan laifin da “ƙalilan daga cikin masu laifi” suka aikata ya “saba ka’ida,” inda ya ƙara da cewa “dukkan hukumomin gwamnati dole su ɗauki mataki mai ƙarfi don kawar da wannan dabi’a.”
Babban hafsan sojin Isra’ila, Laftanar Janar Eyal Zamir, ya goyi bayan suka da Herzog ya yi, yana mai cewa rundunar soji “ba za ta lamunci ayyukan wasu ’yan ƙalilan masu laifi da ke bata sunan jama’ar da ke bin doka ba.”
Sakataren Janar na Majalisar Dinkin Duniya (UN), Antonio Guterres, a ranar Alhamis, ya la’anci harin da Yahudawan masu haramtattun gidajen suka kai kan masallaci a yankin wanda Isra’ila ta mamaye.
Tashin hankali daga Yahudawa masu ra’ayin rikau kan Falasɗinawa a yankin ya ƙaru tun bayan fara yaƙin Gaza a watan Oktoban 2023, wanda aka fara bayan hare-haren da Hamas ta jagoranta kan Isra’ila.
Tun daga lokacin, an samu ƙaruwar hare-haren da ke haddasa mutuwa tsakanin Falasɗinawa da sojojin Isra’ila a yankin na Yammacin Kogin na Jodan.
Rundunar sojin Isra’ila na yawan fuskantar zargi kan gazawarta wajen ɗaukar mataki mai ƙarfi kan tashin hankalin da Yahudawa ke haddasawa.